Close Menu
  • Home
  • News
    • National
    • International
  • Asrah 24 TV
  • Education
  • Health
  • Podcast
  • Politics
  • Sports
  • More
    • Agriculture
    • Business
    • Climate Changes
    • Culture
    • Environment
    • Entertainment
    • Opinion
    • Religious
    • Security
    • Videos
Facebook X (Twitter) YouTube WhatsApp Telegram
Facebook X (Twitter) WhatsApp Telegram
ASRAH 24 MEDIA
Subscribe
  • Home
  • News
    1. National
    2. International
    3. View All

    KOTU TA SAMU MACE DA LAIFIN YUNKURIN KASHE ƳAR SHEKARA 9 BAYAN TA YAUDARE TA ZUWA DAJI

    June 26, 2026

    KOTU TA KI SAKIN SOWORE, TA DAGE YANKE HUKUNCI ZUWA 30 GA YUNI

    June 24, 2026

    Sarkin Ilorin Ya Taya Musulmi Murnar Sabuwar Shekarar Hijira, Ya Yi Kiran Hadin Kai

    June 16, 2026

    Ranar Dimokuradiyya: SDP Ta Bukaci Shugabanni Su Yi Mulki Da Gaskiya Da Kishin Kasa

    June 12, 2026

    📰 Labarin Yanar Gizo (Hausa Version): Kaduna Pilgrims Board Ya Tabbatar An Yi Hadaya Ga Duk Masu Biyan Kuɗi

    June 9, 2026

    Najeriya Ta Fuskanci Limit na Visa zuwa Amurka – 3 Mako Kaɗai!

    July 9, 2025

    Gwamnatin Tarayya Tare da Faransa Za Su Inganta ICT a Jami’o’in Najeriya da Tallafin Naira Biliyan 38

    July 4, 2025

    Zafin Rana Mai Tsanani Ya Ɓarke a Turai: Matsalar Heat Dome

    June 30, 2025

    July 3, 2026

    Majalisar Iran Ta Bukaci Jama’a Su Halarci Jana’izar Jagoran Addini Domin Nuna Hadin Kai

    July 2, 2026

    Kalaman Remi Tinubu kan sana’ar ƙosai da gasasshen masara sun jawo ce-ce-ku-ce a kafafen sada zumunta

    June 26, 2026

    Gwamnatin Tarayya ta yabawa jakadan Najeriya bayan sakin ‘yan Najeriya da aka tsare a Côte d’Ivoire

    June 26, 2026
  • Asrah 24 TV
  • Education

    NELFUND Na Binciken Makarantu 34 Kan Rashin Mayar Wa Dalibai Kudin Makaranta

    July 6, 2026

    ‘Yar Najeriya Ta Kammala Karatun Likitanci a Rasha da Makin 4.90 CGPA

    July 6, 2026

    Portable Ya Ce Zai Koma Makaranta Domin Kammala Karatunsa

    July 6, 2026

    Gwamnatin Tarayya Za Ta Rika Gudanar da Gwajin Kwarewar Dalibai Duk Bayan Shekaru Uku – Alausa

    July 3, 2026

    Gwamnatin Tarayya Ta Shirya Sauya Kakin NYSC Da Tufafin Adire

    July 2, 2026
  • Health

    Majalisar Dattawa Ta Gabatar Da Kudirin Kirkirar Tsarin Lafiya Na Zamani Zuwa Karatu Na Biyu

    July 8, 2026

    “Ba Abu Ne Mai Sauƙi Ba” – Wata Uwar da Ta Yi Surrogacy Ta Bayyana Kalubalen da Ta Fuskanta

    July 7, 2026

    Jinyar Mace Ta Karya Al’adar Addinin Buddha Domin Ceto Rayukan Sufaye Bayan Mummunan Hatsari

    July 3, 2026

    Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alkawarin Karfafa Hadin Gwiwa Da Cibiyoyin Bincike Domin Dakile Barkewar Cututtuka

    July 2, 2026

    TETFund ta ƙalubalanci masana kimiyya su gaggauta samar da rigakafin cutar Lassa Fever na farko a Najeriya

    June 30, 2026
  • Podcast
  • Politics

    Tinubu Ya Aika Sunan Lamido Yuguda Domin Shugabancin AMCON

    July 8, 2026

    Majalisar Dattawa Ta Amince Da Nada Dr. Zainab Marwa A Hukumar NDDC

    July 8, 2026

    Rigima Ta Barke A Majalisar Wakilai Kan Bukatar A Gayyaci Tinubu

    July 8, 2026

    Mai Yiwuwa Ba Zan Kai Ga Tsayawa Takarar 2027 Ba cewar Peter Obi

    July 8, 2026

    An Binciki PFIPC: Adeyemi Ya Sha Alwashin Bai Wa ICPC Hadin Kai

    July 8, 2026
  • Sports

    Messi Ya Kafa Sabon Tarihi A Gasar Kofin Duniya Ta FIFA

    July 8, 2026

    Masar Ta Bukaci FIFA Ta Hukunta Alkalan Wasanta Da Argentina

    July 8, 2026

    Yusuf Alli Ya Bukaci ‘Yan Wasan Najeriya Su Zama Masu Ladabi Gabanin Wasannin Commonwealth 2026

    July 6, 2026

    Kwara United Ta Sanya Ranar Komawa Sansani Gabanin Sabon Kakarar NPFL

    July 2, 2026

    Coco Gauff Ta Bayyana Yadda Gwajin Hana Amfani da Kwayoyin Kara Kuzari Ya Taba Sanya Ta Yin Kuka

    July 2, 2026
  • More
    • Agriculture
    • Business
    • Climate Changes
    • Culture
    • Environment
    • Entertainment
    • Opinion
    • Religious
    • Security
    • Videos
ASRAH 24 MEDIA
Home » Kotu Ta Yi Watsi Da Bukatar Yahaya Bello Na Kalubalantar Hurumin Shari’ar Zargin Badakalar N110.4bn
News

Kotu Ta Yi Watsi Da Bukatar Yahaya Bello Na Kalubalantar Hurumin Shari’ar Zargin Badakalar N110.4bn

Asrah24 MediaBy Asrah24 MediaJune 16, 20262 Mins Read
Facebook Twitter WhatsApp
Yahaya Bello 671x536

Babbar Kotun Tarayya ta Babban Birnin Tarayya (FCT) da ke zama a Maitama, Abuja, ta yi watsi da bukatar tsohon gwamnan Jihar Kogi, Yahaya Adoza Bello, wadda ke neman a soke shari’ar zargin badakalar kudade ta Naira biliyan 110.4 da Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa (EFCC) ke yi masa.

Yahaya Bello na fuskantar shari’a tare da Umar Shuaibu Oricha da Abdulsalami Hudu kan tuhume-tuhume guda 16 da suka shafi karya amana da kuma halasta kudaden da ake zargin an samu ta haramtacciyar hanya.

A cikin bukatar da ya gabatar, Bello ya kalubalanci hurumin kotun FCT na sauraron karar, yana mai cewa akwai wata makamanciyar shari’a da ke gaban Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja.

Sai dai lauyan masu gabatar da kara, Kemi Pinheiro (SAN), ya bayyana cewa bukatar ba ta da tushe a shari’a, kuma an gabatar da ita ne domin jinkirta ci gaban shari’ar.

A hukuncin da Mai Shari’a Maryanne Anenih ta yanke, kotun ta amince da hujjojin masu gabatar da kara, inda ta tabbatar da cewa tana da hurumin sauraron karar. Ta kuma yi watsi da bukatar Yahaya Bello da wata irin ta wanda ake kara na uku, tana mai cewa dukkaninsu ba su da wani ingantaccen dalili.

Bayan yanke hukuncin, kotun ta umarci a ci gaba da sauraron karar, inda masu gabatar da kara suka gabatar da shaidu na 16 da na 17.

Shaidan farko, Baba Isah Usman Baffa, ya shaida wa kotu cewa Ali Bello ya sayi wani shago a Sherrif Plaza da ke Abuja kan Naira miliyan 66, inda aka biya Naira miliyan 40 da farko sannan aka kammala sauran kudin daga baya.

Shi kuwa shaidan na 17,shehu Bello, ya bayyana yadda ya taimaka wajen saye da sayar da kadarori daban-daban ga Ali Bello da wasu ‘yan uwansa a wurare kamar Guzape, Maitama da Wuse II a Abuja, inda ya bayyana darajar wasu kadarorin da suka kai daruruwan miliyoyin naira.

Daga bisani, Mai Shari’a Anenih ta dage sauraron karar zuwa ranar 17 ga Yuni, 2026 domin ci gaba da gabatar da shaidu da sauraron shari’ar.

Share. Facebook Twitter Telegram WhatsApp
Previous ArticleMakinde Ya Ba da Tabbacin Ceto Dalibai da Malaman da Aka Sace a Oyo
Next Article An Kashe Jami’an Tsaro 3 a Harin NIPSS, Dangote Ya Rage Farashin Fetur da N75

Related Posts

July 3, 2026

Majalisar Iran Ta Bukaci Jama’a Su Halarci Jana’izar Jagoran Addini Domin Nuna Hadin Kai

July 2, 2026

Kalaman Remi Tinubu kan sana’ar ƙosai da gasasshen masara sun jawo ce-ce-ku-ce a kafafen sada zumunta

June 26, 2026

Gwamnatin Tarayya ta yabawa jakadan Najeriya bayan sakin ‘yan Najeriya da aka tsare a Côte d’Ivoire

June 26, 2026
Add A Comment
Leave A Reply Cancel Reply

Latest Posts

Ministan Tsaro Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Harbe ’Yan Ta’adda Ba Tare Da Jira Umarni Ba

July 8, 2026

Tinubu Ya Aika Sunan Lamido Yuguda Domin Shugabancin AMCON

July 8, 2026

Messi Ya Kafa Sabon Tarihi A Gasar Kofin Duniya Ta FIFA

July 8, 2026

Sabon Mamban Kwamitin TETFund Ya Yi Alƙawarin Yin Aiki Cikin Gaskiya

July 8, 2026

Majalisar Dattawa Ta Gabatar Da Kudirin Kirkirar Tsarin Lafiya Na Zamani Zuwa Karatu Na Biyu

July 8, 2026
Connect with us
  • Facebook
  • Twitter
  • YouTube
  • WhatsApp
  • Instagram
  • TikTok
Top Posts
Advertisement
© 2026 ASRAH 24 MEDIA. Developed by ENGRMKS & CO..
  • Home
  • About Us
  • Contact Us
  • Privacy Policy

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.