Gwamnan Jihar Oyo, Seyi Makinde, ya tabbatar wa al’ummar jihar cewa za a ceto dalibai da malamai da aka sace, yana mai cewa gwamnati na yin duk mai yiwuwa domin ganin an kubutar da su cikin koshin lafiya.
Makinde ya bayyana hakan ne yayin da yake ganawa da fitaccen mai tasiri a kafafen sada zumunta, VeryDarkMan, da wasu masu zanga-zanga a Fadar Gwamnatin Jihar Oyo, kamar yadda wani bidiyo da ke yawo ya nuna a ranar Talata.
Da yake magana kan lamarin, gwamnan ya ce shi ma abin ya dame shi matuka, musamman ganin cewa wadanda aka sace sun hada da yara kanana na makarantar firamare da na renon yara, wadanda suka shafe sama da wata guda a hannun masu garkuwa da mutane.
“Ni ma ina cikin damuwa saboda ina da yara nawa. Abin da ya faru da yaranmu ya dame ni sosai. Yanzu wata guda da kwana daya kenan da sace su,” in ji Makinde.
Ya bayyana cewa ba zai iya bayyana cikakkun bayanai kan aikin ceto da ake gudanarwa ba saboda dalilan tsaro, amma ya tabbatar da cewa jami’an tsaro na aiki tukuru domin ganin an kubutar da su lafiya.
Gwamnan ya ce wannan shi ne karo na farko da aka sace yara kanana masu karancin shekaru a irin wannan yanayi a Najeriya, lamarin da ya sa aikin ceton ya zama na musamman.
Makinde ya kuma jaddada cewa gwamnati na kokarin tabbatar da cewa babu wani daga cikin yaran da zai rasa ransa yayin aikin ceto.
“Ba na son rasa ko daya daga cikin yaran nan. Ina ba ku tabbacin cewa ni a matsayina na gwamna, da yardar Allah, za a kubutar da su,” ya ce.
Har ila yau, ya bayyana cewa gwamnati na tattaunawa da masu garkuwa da mutanen domin tabbatar da rayuwar yaran, yana mai cewa wannan mataki ne na musamman da yanayin da ake ciki ya tilasta dauka.
Ya kara da cewa da zarar an kubutar da yaran, gwamnati za ta dauki matakan da za su hana irin wannan lamari sake faruwa a jihar.
