Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, ya taya al’ummar Musulmi a Najeriya da ma duniya baki daya murnar shiga sabuwar shekarar Musulunci ta 1448AH, wadda ta zo daidai da ranar Talata, 16 ga Yuni, 2026.
Yayin da Musulmi ke fara sabuwar shekarar Hijira, shugaban ya yi tsokaci kan muhimmancin Hijira daga Makka zuwa Madina, wadda ta zama farkon kalandar Musulunci. Ya ce darussan Hijira da suka hada da sadaukarwa, sabuntawa, hakuri da kuma yarda da tsarin Allah suna da matukar muhimmanci wajen gina kasa mai zaman lafiya, adalci da ci gaba.
A cikin wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Bayo Onanuga, ya fitar, Tinubu ya bukaci ‘yan Najeriya, musamman Musulmi, da su yi amfani da wannan lokaci wajen sabunta kudurinsu na zama nagartattun ‘yan kasa.
Ya kuma jaddada muhimmancin nuna kyautatawa, hakuri da juna, gaskiya da kuma sadaukar da kai wajen aiki domin karfafa hadin kai, tsaro da ci gaban kasa.
Shugaban ya yi addu’ar Allah Ya sanya sabuwar shekarar Musulunci ta zo da albarka, zaman lafiya da wadata ga kowane gida, tare da ci gaba da shiryar da Najeriya kan tafarkin ci gaba da nasara.
