Gwamnan Jihar Benue, Hyacinth Alia, ya yaba wa Majalisar Wakilai kan amincewa da kudirin dokar kafa rundunar ‘yan sandan jihohi, yana mai cewa matakin zai taimaka matuka wajen karfafa tsaro a Najeriya.
Alia ya bayyana hakan ne a sakonsa na Ranar Dimokuradiyya ta 2026, inda ya ce kudirin ya nuna an fahimci muhimmancin samar da tsarin tsaro na cikin gida da zai iya magance matsalolin tsaro da ke addabar jihohi daban-daban.
Ya ce ‘yan majalisar sun nuna jajircewa da hangen nesa wajen daukar matakin da zai taimaka wajen kare rayuka da dukiyoyin al’umma.
“Ya kamata ‘yan Najeriya su dauki wannan ci gaba a matsayin wani muhimmin gyara da aka yi domin inganta tsaro da kare jama’a,” in ji gwamnan.
Alia ya bayyana cewa idan aka samar da tsauraran ka’idoji da tsarin sa ido, rundunar ‘yan sandan jihohi za ta taimaka wajen tattara bayanan sirri cikin sauri da kuma daukar matakan gaggawa kan barazanar tsaro.
Ya kara da cewa gwamnatinsa ta dauki matakai da dama wajen yaki da rashin tsaro, ciki har da samar da motocin aiki sama da 150, babura 600, da kuma kafa rundunar Benue State Civil Protection Guards da Anyam Nyor Joint Task Force.
A cewarsa, wadannan kokari sun taimaka wajen rage matsalolin tsaro da kuma dawo da zaman lafiya a wasu yankunan jihar.
Gwamnan ya bayyana amincewa da kudirin kafa ‘yan sandan jihohi a matsayin wani babban ci gaba a kokarin samar da Najeriya mai zaman lafiya da tsaro ga kowa.
