Shugaban Shirin Afuwar Shugaban Kasa (PAP), Dennis Otuaro, ya yabawa Shugaba Bola Ahmed Tinubu bisa irin ci gaban da ake samu a yankin Neja Delta, yana mai cewa yankin na amfana da ribar dimokuradiyya a karkashin gwamnatinsa.
A cikin sakon da ya fitar domin bikin Ranar Dimokuradiyya ta 12 ga Yuni, Otuaro ya bayyana cewa ranar tana da muhimmanci a tarihin siyasar Najeriya domin tana wakiltar gwagwarmayar tabbatar da sahihin zabe da shugabanci nagari.
Ya kuma karrama marigayi Chief Moshood Kashimawo Olawale Abiola da sauran jaruman gwagwarmayar 12 ga Yuni, yana mai cewa sadaukarwar da suka yi ce ta taimaka wajen dawo da mulkin dimokuradiyya a shekarar 1999.
Otuaro ya ce gwamnatin Tinubu na ci gaba da karfafa cibiyoyin dimokuradiyya tare da bai wa jama’a damar shiga harkokin shugabanci.
A cewarsa, karin tallafin da gwamnatin tarayya ta bai wa PAP ya taimaka wajen fadada shirye-shiryen bayar da guraben karatu, koyon sana’o’i da tallafa wa matasa a yankin Neja Delta.
Ya bayyana cewa sama da dalibai 8,235 ne ke cin gajiyar guraben karatu na cikin gida da na kasashen waje karkashin shirin.
Shugaban PAP ya kuma yi nuni da manyan ayyukan raya kasa da gwamnatin Tinubu ke gudanarwa, ciki har da titin Lagos zuwa Calabar, kafa Hukumar Raya Yankin Kudu maso Kudu, Jami’ar Muhalli da Fasaha ta Ogoniland da kuma Jami’ar Harkokin Ruwa ta Najeriya da ke Okerenkoko.
Dangane da matsalar tsaro, Otuaro ya bukaci al’umma su ci gaba da bai wa jami’an tsaro hadin kai domin tabbatar da zaman lafiya da ci gaba.
Ya kuma yi kira ga matasa da tsoffin masu tayar da kayar baya a yankin da su ci gaba da rungumar zaman lafiya, yana mai cewa babu ci gaba mai dorewa ba tare da kwanciyar hankali ba.
A karshe, Otuaro ya bukaci al’ummar Neja Delta su ci gaba da mara wa Shugaba Tinubu baya, yana mai cewa ayyukan da ya gudanar a yankin sun nuna irin kulawa da soyayyar da yake da ita ga yankin da mutanensa.
