Sanatan da ke wakiltar Edo ta Tsakiya a Majalisar Dattawa, Joseph Ikpea, ya yabawa Gwamnan Jihar Edo, Monday Okpebholo, bisa matakin gaggawa da ya dauka na rufe wasu makarantu domin kare dalibai daga yiwuwar harin masu garkuwa da mutane.
Gwamna Okpebholo ya bayar da umarnin rufe makarantu uku da ke karamar hukumar Akoko Edo bayan samun bayanan sirri daga Hukumar Tsaro ta DSS cewa wasu ‘yan bindiga na shirin kai hari tare da sace dalibai a yankin Edo ta Arewa.
Makarantun da abin ya shafa sun hada da Ososo Grammar School, Ososo Comprehensive High School da kuma Makeke Secondary School.
A cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Alhamis, Sanata Ikpea ya ce matakin da gwamnan ya dauka ya nuna shugabanci nagari da kuma fifita rayuka da lafiyar al’umma sama da komai.
Ya bayyana cewa duk da cewa rufe makarantu a wannan lokaci na iya jefa dalibai cikin matsala kasancewar ana gudanar da wasu muhimman jarabawa, amma ya fi dacewa a dauki matakin kariya maimakon jiran aukuwar abin da zai jefa iyaye da dalibai cikin hadari.
Sanatan ya kuma yi kira ga al’ummar Najeriya, musamman mazauna Edo ta Tsakiya, da su kasance masu sanya ido tare da kai rahoton duk wani motsi ko mutum da suke zargin baƙo ne ga jami’an tsaro.
Ya kara da cewa matsalar tsaro ba ta shafi gwamnati kadai ba, illa dukkan ‘yan kasa suna da rawar da za su taka wajen tabbatar da zaman lafiya da kare al’ummarsu.
Ikpea ya yabawa DSS da sauran hukumomin tsaro bisa hadin gwiwar da suke yi da gwamnatin jihar wajen dakile ayyukan masu garkuwa da mutane da sauran miyagun laifuka.
Rahotanni sun nuna cewa DSS ta gano wata makarkashiyar sace dalibai a wasu makarantu na Edo ta Arewa, lamarin da ya sa gwamnatin jihar ta dauki matakin rufe makarantun domin kauce wa duk wani hadari.
