Gwamnatin Jihar Neja ta kaddamar da sabuwar Hukumar Kula da Asibitoci da Cibiyoyin Lafiya Masu Zaman Kansu (NISPHFA), domin inganta sa ido kan harkokin kiwon lafiya masu zaman kansu da kuma tabbatar da ingantaccen aikin jinya a fadin jihar.
Da yake jawabi yayin kaddamar da hukumar a Minna, Shugaban Hukumar kuma Babban Darakta, Dakta Abdullahi Suleiman, ya ce an kafa hukumar ne domin tabbatar da ingancin ayyukan lafiya, kare lafiyar marasa lafiya da kuma tabbatar da bin dokoki da ka’idoji a bangaren kiwon lafiya mai zaman kansa.
Ya bayyana cewa hukumar za ta kare muradun marasa lafiya, ta kara inganta matakan aiki da kuma tabbatar da gaskiya da rikon amana a tsakanin masu gudanar da asibitoci masu zaman kansu.
A cewarsa, manufar hukumar ita ce ta zama daya daga cikin manyan hukumomin kula da harkokin lafiya a Najeriya, wacce za ta samar da tsarin kiwon lafiya mai zaman kansa da ya dace da ka’idojin kasa da kasa.
Suleiman ya ce an bai wa hukumar ikon yin rajista, sa ido, dubawa da kuma tantance dukkan cibiyoyin lafiya masu zaman kansu da ke aiki a jihar domin tabbatar da bin ka’idojin da aka amince da su.
Ya kara da cewa hukumar za ta kula da bayar da lasisi ga cibiyoyin lafiya, tsara ka’idojin ma’aikata, gine-gine, kayan aiki da ayyukan jinya, tare da gudanar da bincike da daukar matakan hukunci idan an samu sabawa dokoki.
Shugaban hukumar ya bayyana cewa an riga an samar da ka’idojin rajista ga rukuni 20 na cibiyoyin lafiya masu zaman kansu, tare da kaddamar da tsarin rajista na zamani ta hanyar fasaha.
Ya kuma ce hukumar ta riga ta tuntubi fiye da cibiyoyin lafiya masu zaman kansu 1,000 a kananan hukumomi 25 na jihar.
Suleiman ya kara da cewa an samar da hadin gwiwa da hukumomin tsaro da sauran hukumomin sa ido domin tabbatar da bin ka’idoji yadda ya kamata.
A nasa bangaren, Kwamishinan Lafiya na Jihar Neja, Dakta Murtala Bagana, ya bayyana kafa hukumar a matsayin babban ci gaba a shirin gwamnatin jihar na gyaran tsarin kiwon lafiya.
Ya ce wannan mataki ya yi daidai da manufar Gwamna Umaru Bago ta New Niger Agenda da kuma tsarin gyaran lafiya na THRIVE, wanda ke mayar da hankali kan karfafa shugabanci, inganta ababen more rayuwa, tabbatar da gaskiya da fadada samun ingantaccen kiwon lafiya.
Gwamna Umaru Bago, wanda shugaban ma’aikatan jihar Alhaji Abubakar Sadiq ya wakilta, ya ce kafa hukumar na nuna kudirin gwamnatinsa na gina hukumomi masu anfani ga jama’a.
Ya yaba wa Ma’aikatar Lafiya bisa kokarin da take yi wajen aiwatar da sauye-sauyen da za su inganta lafiyar al’umma da kare marasa lafiya.
