Rahotanni sun nuna cewa wurin da aka tsara gudanar da taron, wato Moshood Abiola National Stadium a Abuja, ya kasance babu kowa a lokacin da aka tsara fara taron a ranar Talata.
Wani dan jarida daga TV Platinum ya bayyana cewa wurin ya kasance shiru kuma babu alamun shiri.
“Muna nan a filin wasa na kasa a Abuja inda ake sa ran bangaren Nafiu Bala na ADC zai gudanar da taronsa na kasa. Amma kamar yadda kuke gani, wurin babu kowa, babu shirye-shirye, babu wakilai, ko ‘yan jam’iyya,” in ji rahoton.
Rahoton ya kara da cewa har ma sashen velodrome ya kasance a kulle, lamarin da ya kara nuna cewa taron bai fara ba.
RIKICIN SHUGABANCI A ADC
Wannan lamari ya kara bayyana rikicin shugabanci da ke ci gaba a cikin jam’iyyar ADC, inda bangarori daban-daban ke ikirarin mallakar tsarin jam’iyyar gabanin zaben 2027.
A baya, bangaren Nafiu Bala ya kaddamar da ranar 21 ga Afrilu, 2026 a matsayin ranar taronsu, kwanaki kadan bayan wani bangare da David Mark ke jagoranta ya gudanar da nasa taron a ranar 14 ga Afrilu.
ZARGIN KETA DOKA
Nafiu Bala ya bayyana cewa taron bangaren David Mark “ba shi da inganci”, yana zargin cewa an keta hukuncin kotu da kuma yin abubuwan da ba su da tushe na doka.
Ya kuma ce hukumar INEC ba ta halarci taron ba, abin da ya nuna cewa ba shi da amincewar hukuma.
MATSAKAN KOTU DA INEC
Rikicin jam’iyyar ya riga ya kai kotu, inda ake ci gaba da sauraron shari’a a gaban Mai Shari’a Emeka Nwite.
Haka kuma, INEC ta bayyana cewa ba za ta amince da bangaren kowane daga cikin rikicin ba, tana mai cewa tana bin umarnin kotu na “status quo ante bellum”.
INEC ta ce ba za ta shiga ko lura da tarukan kowanne bangare ba har sai kotu ta yanke hukunci na karshe.
