Keir Starmer, Firayim Ministan Birtaniya, ya bayyana a ranar Litinin cewa kasar sa ba za ta shiga rikicin yaki tsakanin Iran da wasu kasashe ba, kuma ba za ta goyi bayan toshe hanyar ruwa ta Strait of Hormuz ba.
A wata hira da BBC Radio 5 Live, Starmer ya ce duk wata matsin lamba da ake yi wa Birtaniya, ba za a ja ta cikin yaki ba.
Ya ce:
“Ba mu goyon bayan toshe hanyar ruwa. A ganina yana da matukar muhimmanci a sake bude Strait of Hormuz gaba daya, kuma wannan shi ne abin da muke kokari akai a kwanakin baya, kuma za mu ci gaba da yin hakan.”
Firayim Ministan ya kara da cewa Birtaniya na da jiragen yaki masu aikin share nakiyoyi a yankin, amma ya ki bayyana cikakken bayanin ayyukan sojoji.
Ya bayyana cewa karfin sojan Birtaniya a yankin ya fi karkata ne wajen tabbatar da cewa an sake bude hanyar ruwa domin zirga-zirgar kasuwanci ta ci gaba ba tare da matsala ba.
Wannan bayanin na zuwa ne bayan rahotanni daga sojojin Amurka da suka ce za su fara matakin hana jiragen ruwa shiga da fita daga tashoshin Iran, bayan tattaunawar zaman lafiya ta kasa cimma matsaya.
