Sabon jakadan Najeriya zuwa Majalisar Ɗinkin Duniya (UN), Jimoh Ibrahim, ya bayyana cewa Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu na tattaunawa da manyan ƙasashe kamar Amurka, Birtaniya da kuma Türkiye domin nemo mafita ga matsalolin tsaro da ke addabar Najeriya.
Ibrahim ya bayyana hakan ne a ranar Juma’a a birnin New York lokacin da ya isa domin fara aikinsa a matsayin wakilin dindindin na Najeriya a Majalisar Ɗinkin Duniya.
Ya ce gwamnatin Najeriya ba ta takaita ga ƙasa guda ba wajen neman taimako, sai dai tana buɗe ƙofa ga duk wata ƙasa da za ta iya bayar da gudummawa wajen magance matsalolin tsaro, musamman rikicin Boko Haram.
A cewarsa:
“Najeriya ƙasarmu ce. Muna iya fuskantar matsaloli kamar Boko Haram, amma muna shiga hulɗa da ƙasashe da dama domin shawo kansu.”
Ya ƙara da cewa:
“Ba mu dogara da ƙasa ɗaya ba. Muna son ƙasashe da dama su taimaka mana. Shugaban ƙasa yana tattaunawa da Amurka, Türkiye, sannan daga London muka fito – Birtaniya ma za ta taimaka.”
Ibrahim ya jaddada cewa ƙasashe da dama a duniya sun taɓa fuskantar irin waɗannan matsaloli, yana misali da harin ta’addanci na Satumba 11 a Amurka.
Ya kuma bayyana cewa Shugaba Tinubu ya tura shi Majalisar Ɗinkin Duniya ne domin haɗa kan ƙasashen duniya su mara wa Najeriya baya wajen shawo kan matsalolin tsaro.
Tsohon sanatan da ya wakilci jihar Ondo ya ƙara da cewa dole ne Najeriya ta ci gaba da kasancewa ƙasa ɗaya mai cikakken iko.
A ƙarshe ya ce:
“Dole ne Shugaban ƙasa ya yi nasara. Najeriya ƙasa ɗaya ce mai cikakken ‘yanci kuma dole ta ci gaba da kasancewa haka.”
