Jam’iyyar APC reshen Jihar Osun ta yi watsi da umarnin Gwamna Ademola Adeleke na fara gyaran Gadar Olaiya Flyover da ke Osogbo, tana mai cewa gadar tana cikin kyakkyawan yanayi kuma ba ta da wata matsala da ke buƙatar gyara.
Tun da farko, Gwamna Adeleke ya umarci Ma’aikatar Ayyuka ta jihar da ta fara aikin gyaran gadar kafin kaddamar da sabuwar Gadar Okefia Flyover da gwamnatinsa ta gina. Ya ce gwamnati tana da alhakin kula da dukkan kadarorin jama’a, ba tare da la’akari da gwamnatin da ta aiwatar da su ba.
Sai dai mai magana da yawun APC a jihar, Kola Olabisi, ya ce shirin gyaran ba shi da wani dalili na zahiri. Ya zargi gwamnatin Adeleke da ƙoƙarin kashe kuɗin al’umma ba tare da buƙata ba, yana mai cewa babu wata ƙungiyar injiniyoyi da ta taɓa bayyana cewa gadar na da matsala tun bayan kaddamar da ita kimanin shekaru huɗu da suka gabata.
Lamarin ya ƙara nuna rashin jituwa tsakanin gwamnatin jihar da jam’iyyar APC, musamman bayan sabanin da ya biyo bayan ziyarar Sufeto Janar na ‘Yan Sanda, Olatunji Disu, zuwa jihar.
