Gwamnatin Tarayya ta sake jaddada aniyarta ta kawar da cutar Peste des Petits Ruminants (PPR), wata ƙwayar cuta mai saurin yaɗuwa da ke kashe tumaki da awaki, kafin shekarar 2030.
Babbar Sakatariyar Ma’aikatar Bunƙasa Kiwo ta Tarayya, Chinyere Akujobi, ce ta bayyana hakan yayin taron masu ruwa da tsaki kan sabunta tsarin ƙasa na yaƙi da cutar PPR da aka gudanar a Abuja.
Ta ce gwamnati za ta ci gaba da ƙarfafa sa ido kan cutar, gudanar da allurar rigakafi ga dabbobi, binciken barkewar cututtuka da kuma haɗin gwiwa da ƙasashen maƙwabta domin cimma burin kawar da cutar.
Akujobi ta bayyana cewa kawar da PPR ba wai kare lafiyar dabbobi kaɗai ba ne, har ila yau yana da muhimmanci wajen rage talauci, bunƙasa rayuwar al’ummomin karkara, ƙara yawan amfanin kiwo da faɗaɗa kasuwancin dabbobi.
Ta ce Najeriya na da tumaki da awaki sama da miliyan 200, wanda ya sa ya zama wajibi a ƙarfafa matakan kariya saboda ƙasar na mu’amala da ƙasashe maƙwabta kamar Jamhuriyar Nijar, Benin, Kamaru da Chadi.
A cewarta, sabon tsarin da gwamnati ke shiryawa na shekarun 2026 zuwa 2030 zai haɗa da amfani da sabbin bayanan bincike, taswirar wuraren da cutar ta fi kamari da kuma inganta hanyoyin rigakafi da gwaje-gwaje.
Babban Likitan Dabbobi na Ƙasa, Dr. Samuel Anzaku, ya ce Najeriya ta samu ci gaba wajen yaƙi da cututtukan dabbobi, amma akwai buƙatar sabunta tsarin domin ya dace da manufofin ƙasa da ƙasa na kawar da cutar PPR.
Shi ma wakilin African Union Inter-African Bureau for Animal Resources (AU-IBAR), Dr. Perdita Hilary Lopes, ya ce kawar da cutar PPR zai taimaka wajen bunƙasa kiwo, rage talauci, ƙarfafa tattalin arzikin mata da matasa, da kuma inganta wadatar abinci a nahiyar Afirka.
Gwamnatin Tarayya ta ce za ta ci gaba da aiki tare da Hukumar Abinci da Noma ta Majalisar Dinkin Duniya (FAO), Hukumar Lafiyar Dabbobi ta Duniya (WOAH) da sauran ƙungiyoyin ƙasa da ƙasa domin tabbatar da cewa Najeriya ta zama ƙasa mai ‘yanci daga cutar PPR kafin shekarar 2030
