Close Menu
  • Home
  • News
    • National
    • International
  • Asrah 24 TV
  • Education
  • Health
  • Podcast
  • Politics
  • Sports
  • More
    • Agriculture
    • Business
    • Climate Changes
    • Culture
    • Environment
    • Entertainment
    • Opinion
    • Religious
    • Security
    • Videos
Facebook X (Twitter) YouTube WhatsApp Telegram
Facebook X (Twitter) WhatsApp Telegram
ASRAH 24 MEDIA
Subscribe
  • Home
  • News
    1. National
    2. International
    3. View All

    KOTU TA SAMU MACE DA LAIFIN YUNKURIN KASHE ƳAR SHEKARA 9 BAYAN TA YAUDARE TA ZUWA DAJI

    June 26, 2026

    KOTU TA KI SAKIN SOWORE, TA DAGE YANKE HUKUNCI ZUWA 30 GA YUNI

    June 24, 2026

    Sarkin Ilorin Ya Taya Musulmi Murnar Sabuwar Shekarar Hijira, Ya Yi Kiran Hadin Kai

    June 16, 2026

    Ranar Dimokuradiyya: SDP Ta Bukaci Shugabanni Su Yi Mulki Da Gaskiya Da Kishin Kasa

    June 12, 2026

    📰 Labarin Yanar Gizo (Hausa Version): Kaduna Pilgrims Board Ya Tabbatar An Yi Hadaya Ga Duk Masu Biyan Kuɗi

    June 9, 2026

    Najeriya Ta Fuskanci Limit na Visa zuwa Amurka – 3 Mako Kaɗai!

    July 9, 2025

    Gwamnatin Tarayya Tare da Faransa Za Su Inganta ICT a Jami’o’in Najeriya da Tallafin Naira Biliyan 38

    July 4, 2025

    Zafin Rana Mai Tsanani Ya Ɓarke a Turai: Matsalar Heat Dome

    June 30, 2025

    July 3, 2026

    Majalisar Iran Ta Bukaci Jama’a Su Halarci Jana’izar Jagoran Addini Domin Nuna Hadin Kai

    July 2, 2026

    Kalaman Remi Tinubu kan sana’ar ƙosai da gasasshen masara sun jawo ce-ce-ku-ce a kafafen sada zumunta

    June 26, 2026

    Gwamnatin Tarayya ta yabawa jakadan Najeriya bayan sakin ‘yan Najeriya da aka tsare a Côte d’Ivoire

    June 26, 2026
  • Asrah 24 TV
  • Education

    NELFUND Na Binciken Makarantu 34 Kan Rashin Mayar Wa Dalibai Kudin Makaranta

    July 6, 2026

    ‘Yar Najeriya Ta Kammala Karatun Likitanci a Rasha da Makin 4.90 CGPA

    July 6, 2026

    Portable Ya Ce Zai Koma Makaranta Domin Kammala Karatunsa

    July 6, 2026

    Gwamnatin Tarayya Za Ta Rika Gudanar da Gwajin Kwarewar Dalibai Duk Bayan Shekaru Uku – Alausa

    July 3, 2026

    Gwamnatin Tarayya Ta Shirya Sauya Kakin NYSC Da Tufafin Adire

    July 2, 2026
  • Health

    Majalisar Dattawa Ta Gabatar Da Kudirin Kirkirar Tsarin Lafiya Na Zamani Zuwa Karatu Na Biyu

    July 8, 2026

    “Ba Abu Ne Mai Sauƙi Ba” – Wata Uwar da Ta Yi Surrogacy Ta Bayyana Kalubalen da Ta Fuskanta

    July 7, 2026

    Jinyar Mace Ta Karya Al’adar Addinin Buddha Domin Ceto Rayukan Sufaye Bayan Mummunan Hatsari

    July 3, 2026

    Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alkawarin Karfafa Hadin Gwiwa Da Cibiyoyin Bincike Domin Dakile Barkewar Cututtuka

    July 2, 2026

    TETFund ta ƙalubalanci masana kimiyya su gaggauta samar da rigakafin cutar Lassa Fever na farko a Najeriya

    June 30, 2026
  • Podcast
  • Politics

    Tinubu Ya Aika Sunan Lamido Yuguda Domin Shugabancin AMCON

    July 8, 2026

    Majalisar Dattawa Ta Amince Da Nada Dr. Zainab Marwa A Hukumar NDDC

    July 8, 2026

    Rigima Ta Barke A Majalisar Wakilai Kan Bukatar A Gayyaci Tinubu

    July 8, 2026

    Mai Yiwuwa Ba Zan Kai Ga Tsayawa Takarar 2027 Ba cewar Peter Obi

    July 8, 2026

    An Binciki PFIPC: Adeyemi Ya Sha Alwashin Bai Wa ICPC Hadin Kai

    July 8, 2026
  • Sports

    Messi Ya Kafa Sabon Tarihi A Gasar Kofin Duniya Ta FIFA

    July 8, 2026

    Masar Ta Bukaci FIFA Ta Hukunta Alkalan Wasanta Da Argentina

    July 8, 2026

    Yusuf Alli Ya Bukaci ‘Yan Wasan Najeriya Su Zama Masu Ladabi Gabanin Wasannin Commonwealth 2026

    July 6, 2026

    Kwara United Ta Sanya Ranar Komawa Sansani Gabanin Sabon Kakarar NPFL

    July 2, 2026

    Coco Gauff Ta Bayyana Yadda Gwajin Hana Amfani da Kwayoyin Kara Kuzari Ya Taba Sanya Ta Yin Kuka

    July 2, 2026
  • More
    • Agriculture
    • Business
    • Climate Changes
    • Culture
    • Environment
    • Entertainment
    • Opinion
    • Religious
    • Security
    • Videos
ASRAH 24 MEDIA
Home » Kalaman Remi Tinubu kan sana’ar ƙosai da gasasshen masara sun jawo ce-ce-ku-ce a kafafen sada zumunta
News

Kalaman Remi Tinubu kan sana’ar ƙosai da gasasshen masara sun jawo ce-ce-ku-ce a kafafen sada zumunta

Asrah24 MediaBy Asrah24 MediaJune 26, 20262 Mins Read
Facebook Twitter WhatsApp
remi tinubu 550x536

Uwargidan Shugaban Ƙasa, Sanata Oluremi Tinubu, ta fuskanci suka da martani mabambanta a kafafen sada zumunta bayan ta bukaci ‘yan Najeriya su rungumi ƙananan sana’o’i kamar sayar da ƙosai, gasasshen masara da ƙuli-ƙuli domin samun abin dogaro.

Da take zantawa da wakilan fadar shugaban ƙasa bayan taron kwata na biyu na shirin Renewed Hope Initiative (RHI) tare da matan gwamnoni a Abuja, Remi Tinubu ta ce irin waɗannan sana’o’i ba sa buƙatar kuɗi masu yawa kafin a fara su.

Ta bayyana cewa masu cin gajiyar shirin ba rance ake ba su ba, sai dai tallafin kuɗi (grant) domin su kafa sana’o’insu da inganta rayuwarsu.

Ta ce, “Muna ƙoƙarin ba mutane fata. Fara sana’ar ƙosai ba ya buƙatar kuɗi masu yawa. Haka ma gasasshen masara ko ƙuli-ƙuli. Ba rance muka ba su ba, tallafi muka ba su.”

Uwargidan shugaban ƙasar ta kuma bayyana wasu ayyukan da shirin Renewed Hope Initiative ya aiwatar, ciki har da tallafa wa bangaren lafiya, noma, ilimi da shirye-shiryen inganta rayuwar al’umma.

A cewarta, ta bayar da gudummawar Naira biliyan biyu domin yaƙi da cutar tarin fuka (tuberculosis), Naira biliyan ɗaya don tallafawa masu fama da cutar sankarar mama, sannan Naira miliyan 500 domin yaƙi da matsalar tamowa a faɗin ƙasar.

Har ila yau, ta ce shirin ya samar da guraben karatu, horaswar fasahar sadarwa (ICT) da tallafin noma domin ƙarfafa marasa galihu.

Remi Tinubu ta buƙaci ‘yan Najeriya kada su yanke ƙauna duk da matsin tattalin arzikin da ake fuskanta, tana mai cewa manufar Renewed Hope Agenda ita ce samar da fata da inganta rayuwar talakawa.

Sai dai kalamanta sun haifar da muhawara a kafafen sada zumunta. Wasu sun soki furucin nata, suna masu cewa ya nuna rashin fahimtar irin wahalhalun tattalin arzikin da jama’a ke ciki, inda suka ce abin da ‘yan Najeriya ke buƙata shi ne samar da ayyukan yi, rage tsadar rayuwa da bunƙasa tattalin arziki.

A gefe guda kuma, wasu sun kare Uwargidan Shugaban Ƙasar, suna cewa babu aibu a kowace irin halalacciyar sana’a, kuma sana’o’in ƙosai, gasasshen masara da ƙuli-ƙuli sun daɗe suna tallafawa dubban iyalai a Najeriya.

Share. Facebook Twitter Telegram WhatsApp
Previous ArticleBangaren Turaki ya kai ƙorafi ga Sufeto Janar na ‘Yan Sanda kan Anyanwu da Abdulrahman
Next Article Tinubu ya amince da kafa Hukumar Fasahar Lafiya da Binciken Bayanai ta Ƙasa

Related Posts

July 3, 2026

Majalisar Iran Ta Bukaci Jama’a Su Halarci Jana’izar Jagoran Addini Domin Nuna Hadin Kai

July 2, 2026

Gwamnatin Tarayya ta yabawa jakadan Najeriya bayan sakin ‘yan Najeriya da aka tsare a Côte d’Ivoire

June 26, 2026

KOTU TA SAMU MACE DA LAIFIN YUNKURIN KASHE ƳAR SHEKARA 9 BAYAN TA YAUDARE TA ZUWA DAJI

June 26, 2026
Add A Comment
Leave A Reply Cancel Reply

Latest Posts

Ministan Tsaro Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Harbe ’Yan Ta’adda Ba Tare Da Jira Umarni Ba

July 8, 2026

Tinubu Ya Aika Sunan Lamido Yuguda Domin Shugabancin AMCON

July 8, 2026

Messi Ya Kafa Sabon Tarihi A Gasar Kofin Duniya Ta FIFA

July 8, 2026

Sabon Mamban Kwamitin TETFund Ya Yi Alƙawarin Yin Aiki Cikin Gaskiya

July 8, 2026

Majalisar Dattawa Ta Gabatar Da Kudirin Kirkirar Tsarin Lafiya Na Zamani Zuwa Karatu Na Biyu

July 8, 2026
Connect with us
  • Facebook
  • Twitter
  • YouTube
  • WhatsApp
  • Instagram
  • TikTok
Top Posts
Advertisement
© 2026 ASRAH 24 MEDIA. Developed by ENGRMKS & CO..
  • Home
  • About Us
  • Contact Us
  • Privacy Policy

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.