Ministan Babban Birnin Tarayya Abuja, , ya tabbatar wa mazauna Abuja cewa ayyukan raya birnin da ake gudanarwa za su ci gaba ba tare da tangarda ba duk da shirye-shiryen siyasar zaben shekarar 2027.
Wike ya bayyana hakan ne a ranar Talata yayin kaddamar da aikin gina hanyoyin gefen titin Southern Parkway daga Arterial Road S20 (Oladipo Diya Way) zuwa Ring Road II, daya daga cikin ayyukan da ake kaddamarwa domin bikin cika shekaru uku na gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.
Ministan ya ce gwamnatin tarayya ta kuduri aniyar sauya fasalin Abuja gaba daya kamar yadda Shugaba Tinubu ya umarta.
A cewarsa, wasu na tambayar ko bayan kammala kaddamar da wadannan ayyuka za a dakatar da sabbin ayyuka saboda fara harkokin siyasa, amma ya ce amsar ita ce a’a.
Wike ya jaddada cewa ko da ana siyasa ko ba a yi ba, gwamnati za ta ci gaba da aiwatar da ayyukan ci gaba domin inganta rayuwar al’umma da kuma kawata babban birnin kasar.
Ya bayyana kwarin gwiwarsa cewa kafin karshen wa’adin farko na Shugaba Tinubu a ranar 29 ga Mayu, 2027, Abuja za ta samu gagarumin sauyi ta fuskar ababen more rayuwa.
A cewarsa, ayyukan da ake yi a fadin Babban Birnin Tarayya na da nufin inganta hanyoyi, saukaka zirga-zirga da kuma bunkasa rayuwar mazauna yankin.
Shugaba Tinubu ya samu wakilci a wajen taron ta hannun Shugaban Jam’iyyar APC na kasa, .
Aikin Southern Parkway na daga cikin manyan ayyukan tituna da gine-gine da Hukumar Babban Birnin Tarayya ke aiwatarwa karkashin jagorancin Wike.
