Fitacciyar ‘yar wasan ƙwallon ƙafa ta Najeriya, , ta musanta wani labari da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke cewa an cire ta daga tawagar Super Falcons saboda wasu dalilai na rashin gaskiya.
A cikin sakon da aka danganta mata a wani shafin Facebook, an ruwaito cewa an cire ta daga tawagar gasar WAFCON mai zuwa bayan ta ƙi amincewa da bukatun wasu jami’ai marasa gaskiya.
Sai dai Plumptre ta fito fili ta karyata wannan labari, tana mai cewa shafin Facebook din ba nata ba ne kuma an kirkiri sakon ne ba tare da izininta ba.
A cikin sakon da ta wallafa a shafinta na Instagram Story a ranar Talata, ta bukaci magoya baya da su kai rahoton shafin na bogi, tana mai cewa shafin yana ci gaba da haddasa matsala duk da cewa yana da alamar tantancewa (verified).
Ta kuma sake jaddada matsayinta a shafinta na X (Twitter), inda ta ce labarin “ba gaskiya ba ne sam”.
Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da labarin ya jawo ce-ce-ku-ce a kafafen sada zumunta, inda mutane suka fara tattaunawa kan dalilin rashin sunanta a jerin ‘yan wasan Super Falcons da za su halarci gasar ta nahiyar Afirka.
Plumptre ta kuma shafe lokaci tana gargadin magoya bayanta kan yawan shafukan Facebook na bogi da ke kwaikwayon sunanta.
