Close Menu
  • Home
  • News
    • National
    • International
  • Asrah 24 TV
  • Education
  • Health
  • Podcast
  • Politics
  • Sports
  • More
    • Agriculture
    • Business
    • Climate Changes
    • Culture
    • Environment
    • Entertainment
    • Opinion
    • Religious
    • Security
    • Videos
Facebook X (Twitter) YouTube WhatsApp Telegram
Facebook X (Twitter) WhatsApp Telegram
ASRAH 24 MEDIA
Subscribe
  • Home
  • News
    1. National
    2. International
    3. View All

    Ranar Dimokuradiyya: SDP Ta Bukaci Shugabanni Su Yi Mulki Da Gaskiya Da Kishin Kasa

    June 12, 2026

    Najeriya Ta Kai Dala $18.4 Biliyan a Cinikayyar Cikin Afirka a 2024

    June 28, 2025

    Afreximbank Ta Ba Najeriya Tallafin $50 Biliyan Don Manyan Ayyuka

    June 28, 2025

    Mutane 28 sun mutu sakamakon gudun wuce sa’a a jihar Ondo- FRSC

    February 2, 2025

    📰 Labarin Yanar Gizo (Hausa Version): Kaduna Pilgrims Board Ya Tabbatar An Yi Hadaya Ga Duk Masu Biyan Kuɗi

    June 9, 2026

    Najeriya Ta Fuskanci Limit na Visa zuwa Amurka – 3 Mako Kaɗai!

    July 9, 2025

    Gwamnatin Tarayya Tare da Faransa Za Su Inganta ICT a Jami’o’in Najeriya da Tallafin Naira Biliyan 38

    July 4, 2025

    Zafin Rana Mai Tsanani Ya Ɓarke a Turai: Matsalar Heat Dome

    June 30, 2025

    Guinness Nigeria Ta Bukaci Hadin Gwiwa Domin Yakar Jabun Kaya A Zamanin AI

    June 12, 2026

    Ranar Dimokuradiyya: SDP Ta Bukaci Shugabanni Su Yi Mulki Da Gaskiya Da Kishin Kasa

    June 12, 2026

    SpaceX Ta Tara Dala Biliyan 75 A Tarihin IPO, Elon Musk Na Daf Da Zama Attajirin Tiriliyan Na Farko

    June 12, 2026

    Taraba Ta Gargadi Jama’a Kan Biyan Haraji a Asusun Banki Na Gwamnati Kadai

    June 11, 2026
  • Asrah 24 TV
  • Education

    NANS Ta Bukaci A Sanya Wakilan Dalibai Cikin Kwamitin Yaki da Ebola

    June 10, 2026

    JAMB Ta Bude Shafin Fitar Da Takardun Jarabawar Mop-Up UTME Ta 2026

    June 8, 2026

    Sojojin Najeriya Sun Yaye Sabbin Paratroopers Bayan Kammala Horon Tsalle Daga Jirgin Sama

    June 5, 2026

    Achievers University Ta Bankado Zargin Damfarar Kudin Makaranta Ta N457.5m

    May 25, 2026

    NYSC ta shawarci iyaye su taimaka wa ‘ya’yansu da karin kudin tafiya

    May 21, 2026
  • Health

    Gwamnati Ta Bukaci Mata Masu Juna Biyu Su Rika Zuwa Asibiti Tun Da Wuri Domin Kula Da Lafiyarsu

    June 11, 2026

    PCN Ta Cafke Mutane Biyar Kan Karya Hatimin Shagunan Magunguna Ba Bisa Ka’ida Ba A Kano

    June 11, 2026

    FCTA Ta Kaddamar Da Sabuwar Hanyar Maganin Fibroid Ba Tare Da Tiyata Ba, Za Ta Yi Wa Mata 100 Magani Kyauta

    June 11, 2026

    Jihar Neja Ta Kaddamar Da Hukumar Kula Da Asibitocin Masu Zaman Kansu

    June 8, 2026

    OYO TA KWANTAR WA MAZAUNA HANKALI KAN CUTAR EBOLA, TA SA MA’AIKATAN LAFIYA CIKIN SHIRI

    June 4, 2026
  • Podcast
  • Politics

    Gwamna Alia Ya Goyi Bayan Kafa ‘Yan Sandan Jihohi, Ya Yabi Majalisar Wakilai

    June 12, 2026

    Dan Takarar Shugaban Kasa Na Action Alliance Ya Bukaci A Kawo Karshen ‘Yan Bindiga Da Satar Mutane

    June 12, 2026

    Ranar Dimokuradiyya: Shugaban PAP Ya Yaba Da Ayyukan Tinubu A Neja Delta

    June 12, 2026

    APC Na Tsoron Karfin Accord A Fadin Osun

    June 12, 2026

    Wasu ‘Yan Najeriya Na Ba ‘Yan Ta’adda Abinci Da Bayanai – Ministan Tsaro

    June 12, 2026
  • Sports

    Messi Shi Ne Mafi Kyawun Dan Wasa Da Na Taba Gani

    June 12, 2026

    Serena Williams Ta Dakatar Da Komawarta Bayan Raunin Abokiyar Wasanta Mboko

    June 11, 2026

    Michel Platini Ya Kai Kara FIFA da Shugabanta Gianni Infantino Kan Zargin Rashawa

    June 9, 2026

    Comoros Ta Tsallaka Wasa Da Super Falcons Bayan Doke Sudan 30–0

    June 9, 2026

    Messi Zai Koma Fili Yayin Da Argentina Ke Kammala Shirye-shiryen Kofin Duniya Na 2026

    June 9, 2026
  • More
    • Agriculture
    • Business
    • Climate Changes
    • Culture
    • Environment
    • Entertainment
    • Opinion
    • Religious
    • Security
    • Videos
ASRAH 24 MEDIA
Home » Majalisar Wakilai Ta Nada Fred Agbedi Sabon Jagoran ‘Yan Adawa
Politics

Majalisar Wakilai Ta Nada Fred Agbedi Sabon Jagoran ‘Yan Adawa

Asrah24 MediaBy Asrah24 MediaJune 12, 20262 Mins Read
Facebook Twitter WhatsApp
01 reps 2 e1686146106154 660x534 (1)

Dan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Sagbama/Ekeremor ta Jihar Bayelsa, Hon. Fred Agbedi, ya zama sabon Jagoran ‘Yan Adawa (Minority Leader) na Majalisar Wakilai.

Agbedi, wanda ke cikin bangaren jam’iyyar PDP karkashin jagorancin Taminu Turaki, ya maye gurbin Hon. Kingsley Chinda bayan ya yi murabus daga mukamin tare da komawa jam’iyyar APC.

Chinda ya sauya sheka ne bayan lashe zaben fidda gwani na gwamnan jihar Rivers na jam’iyyar APC gabanin babban zaben shekarar 2027.

Haka kuma, dan majalisar mai wakiltar Darazo/Ganjuwa a Jihar Bauchi karkashin jam’iyyar APM, Hon. Manu Soro, ya zama Minority Whip, yayin da dan majalisar ADC daga Jihar Sokoto, Hon. Abdulsammad Dasuki, ya zama Mataimakin Jagoran ‘Yan Adawa.

An bayyana sabbin nade-naden ne cikin wata wasika daga ‘yan adawa a majalisar da Kakakin Majalisar Wakilai, Hon. Abbas Tajudeen, ya karanta a zaman majalisar na ranar Alhamis.

A cewar wasikar, an cimma matsaya kan sabbin shugabannin ne ta hanyar yarjejeniya tsakanin ‘yan adawar majalisar.

Wannan ci gaba ya kawo karshen takaddamar da ta dauki makonni ana yi kan wanda zai jagoranci ‘yan adawa bayan kusan ‘yan majalisa 60 daga cikin 80 suka mara wa Hon. Ikenga Ugochinyere baya domin zama Minority Leader.

Sai dai a ranar Laraba, Majalisar Wakilai ta yi gyara ga dokokinta, inda ta haramta wa sabbin ‘yan majalisa masu wa’adi na farko rike mukaman shugabanci a majalisar.

Bayan wannan sauyi, Ugochinyere ya janye takararsa ta neman zama Jagoran ‘Yan Adawa, yana mai cewa ya yi hakan ne domin girmama sabbin dokokin majalisar da kuma tabbatar da hadin kan bangaren ‘yan adawa.

Ya jaddada cewa kungiyar ‘yan adawa za ta ci gaba da aiki tare domin kare dimokuradiyya da kuma tabbatar da zaman lafiya a majalisar.

Share. Facebook Twitter Telegram WhatsApp
Previous ArticleTaraba Ta Gargadi Jama’a Kan Biyan Haraji a Asusun Banki Na Gwamnati Kadai
Next Article Rashin Tallafin Jama’a Na Kara Haddasa Satar Mutane Da Rashin Tsaro A Najeriya – FIWON

Related Posts

Gwamna Alia Ya Goyi Bayan Kafa ‘Yan Sandan Jihohi, Ya Yabi Majalisar Wakilai

June 12, 2026

Dan Takarar Shugaban Kasa Na Action Alliance Ya Bukaci A Kawo Karshen ‘Yan Bindiga Da Satar Mutane

June 12, 2026

Ranar Dimokuradiyya: Shugaban PAP Ya Yaba Da Ayyukan Tinubu A Neja Delta

June 12, 2026

APC Na Tsoron Karfin Accord A Fadin Osun

June 12, 2026
Add A Comment
Leave A Reply Cancel Reply

Latest Posts

Guinness Nigeria Ta Bukaci Hadin Gwiwa Domin Yakar Jabun Kaya A Zamanin AI

June 12, 2026

Ranar Dimokuradiyya: SDP Ta Bukaci Shugabanni Su Yi Mulki Da Gaskiya Da Kishin Kasa

June 12, 2026

Gwamna Alia Ya Goyi Bayan Kafa ‘Yan Sandan Jihohi, Ya Yabi Majalisar Wakilai

June 12, 2026

Dan Takarar Shugaban Kasa Na Action Alliance Ya Bukaci A Kawo Karshen ‘Yan Bindiga Da Satar Mutane

June 12, 2026

Ranar Dimokuradiyya: Shugaban PAP Ya Yaba Da Ayyukan Tinubu A Neja Delta

June 12, 2026
Connect with us
  • Facebook
  • Twitter
  • YouTube
  • WhatsApp
  • Instagram
  • TikTok
Top Posts
Advertisement
© 2026 ASRAH 24 MEDIA. Developed by ENGRMKS & CO..
  • Home
  • About Us
  • Contact Us
  • Privacy Policy

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.