Tsohon Kwamishinan ‘Yan Sandan Jihar Lagos State, Fatai Owoseni, ya janye daga takarar zaben fidda gwani na gwamnan jihar Oyo State karkashin jam’iyyar Accord Party.
Owoseni, wanda ya taba zama mai bai wa gwamnan Oyo, Seyi Makinde shawara kan harkokin tsaro, ya bayyana hakan ne cikin wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na X ranar Talata.
Ya ce wasu abubuwan da suka faru a cikin jam’iyyar sun sanya ba zai iya ci gaba da burinsa na takarar gwamna a karkashin Accord Party ba.
Owoseni ya kuma jajanta wa iyalan wadanda suka mutu da wadanda aka sace a harin da ‘yan ta’adda suka kai a yankin Ogbomoso.
A cewarsa, matsalar tsaro da jihar ke fuskanta ita ce ya kamata ta fi daukar hankalin jama’a a wannan lokaci.
Ya zargi wasu da kutse cikin tsarin jam’iyyar a matakin jiha domin hana burinsa na takarar gwamna samun nasara.
Har ila yau, ya yi zargin cewa ana amfani da rikici da tashin hankali wajen lalata tsarin jam’iyyar da dakatar da tafiyar siyasa.
Owoseni ya ce saboda wadannan matsaloli ne ya yanke shawarar janyewa daga jam’iyyar Accord.
Sai dai ya tabbatar wa magoya bayansa cewa har yanzu yana nan daram wajen neman cigaban jihar Oyo da kuma al’ummar jihar baki daya.
