Wani jigo a jam’iyyar All Progressives Congress a jihar Oyo kuma tsohon shugaban karamar hukumar Oluyole, Kehinde Olaosebikan, ya taya kungiyar Shooting Stars Sports Club murna bayan ta samu damar wakiltar Najeriya a gasar CAF Confederation Cup ta kakar 2026/2027.
A cewar wata sanarwa da ya fitar a ranar Litinin, nasarar ta biyo bayan kammala kakar gasar Nigeria Premier Football League inda kungiyar ta kare a matsayi na uku.
Wannan matsayi ya tabbatar wa kungiyar tikitin shiga gasar nahiyar Afirka bayan shekaru da dama ba ta shiga irin wannan gasa ba.
Olaosebikan ya yaba wa Olubadan na Ibadanland da shugabannin kungiyar da magoya baya bisa rawar da suka taka wajen farfado da martabar 3SC.
Ya kuma ce dole ne a ci gaba da tallafawa kungiyar musamman daga gwamnati da ‘yan kasuwa domin ta samu nasara a matakin nahiyar.
Ya kara da cewa Shooting Stars na daga cikin tsofaffin kji jungiyoyin Najeriya kuma ta taba lashe kofin nahiyar Afirka a shekarar 1976, wanda ya kasance babban tarihi ga kulob din.
