Dan majalisar wakilai mai wakiltar Ekiti Central Federal Constituency II, Biodun Omoleye, ya ƙi amincewa da sakamakon zaben fidda gwani na jam’iyyar All Progressives Congress (APC) da aka gudanar a mazabarsa.
Omoleye ya zargi cewa an samu “manyan kura-kurai, tsoratar da masu kada kuri’a, da kuma hana mutane yin zabe cikin ‘yanci”, lamarin da ya ce ya murde nufin al’ummar yankin.
A cikin wata sanarwa da daraktan yada labaransa, Gloria Femi-Ige, ta fitar a Ado Ekiti a ranar Litinin, ya yi kira ga shugabannin jam’iyyar APC a matakai daban-daban da su shiga tsakani tare da binciken yadda aka gudanar da zaben.
Ya ce idan aka bar sakamakon ya tsaya ba tare da bincike ba, hakan zai iya lalata sahihancin tsarin dimokuradiyyar cikin jam’iyya.
Omoleye ya bayyana zaben da aka gudanar a ranar Asabar a matsayin wanda bai bi ka’ida ba, yana mai cewa an gurbata shi.
Ya ce wasu mazabu sun fuskanci tsoratarwa da hana magoya bayansa yin zabe, inda ya zargi cewa an raba mutane da karfi a wuraren zabe.
“Ba wannan ce dimokuradiyyar da muke bukata ba. An murde ra’ayin jama’a, an kuma yi kokarin rufe bakin masu gaskiya,” in ji shi.
Ya kuma yi kira ga magoya bayansa da su zauna lafiya yayin da yake shirin daukar matakin shari’a domin kalubalantar sakamakon, yana mai kiran lamarin da “satar kuri’a”.
Sakamakon zaben da aka bayyana ya nuna cewa Oladapo Karounwi ya samu kuri’u 6,573, yayin da Omoleye ya samu 1,412, Victor Kolade 2,096, Samuel Olusola 705, sai Olatunde Oyetola 1,202.
Omoleye ya jaddada cewa zai bi dukkan hanyoyin doka domin tabbatar da adalci da kare dimokuradiyya.
