Ƙungiyar ‘yan Najeriya mazauna Afirka ta Kudu (NICASA) ta yi kira ga ƙarin haɗin kan ƙasashen Afirka tare da neman a ɗauki matakai na haɗin gwiwa don dakile matsalolin wariyar baƙi da ke shafar ‘yan Najeriya da sauran ‘yan Afirka a Afirka ta Kudu.
NICASA ta yaba da ƙoƙarin Babban Jakadan Najeriya a Afirka ta Kudu, Ambasada Ninikanwa Okey-Uche, inda ta ce shiga tsakani da ya yi ya taimaka wajen kawo kwanciyar hankali tare da ƙara fata ga ‘yan Najeriya da abin ya shafa.
A cewar ƙungiyar, matakan jakadan sun nuna cewa Najeriya na da ofishin diflomasiyya mai kishin kare ‘yan ƙasa, duk da haka ta bukaci gwamnati ta ƙara ba shi goyon bayan hukumomi.
NICASA ta jaddada aniyarta ta zaman lafiya, bin doka da oda, da kuma tattaunawa mai ma’ana a ƙasar Afirka ta Kudu. Ta kuma shawarci ‘yan Najeriya da ke can da su ci gaba da bin doka, su kasance masu natsuwa, tare da bin hanyoyin diflomasiyya wajen warware matsaloli.
Ƙungiyar ta kuma yi kira ga shugabannin Afirka da su haɗa kai ta hanyar Tarayyar Afirka (AU) da sauran ƙungiyoyin yankuna domin magance abin da ta kira “ƙara yawan rikice-rikicen ƙin baƙi a tsakanin ‘yan Afirka.”
NICASA ta ce wariyar baƙi na sabawa manufar haɗin kan Afirka da ci gaban tattalin arziki, tana mai cewa Afirka ba za ta iya tashi ba idan ‘yan Afirka na ci gaba da rarrabuwar kai.
Ta ƙara da cewa haɗin kai a Afirka ba magana ce kawai ba, wajibi ne domin samun zaman lafiya da ci gaba mai ɗorewa.
A ƙarshe, NICASA ta sake tabbatar da aniyarta ta kare haƙƙi da mutuncin ‘yan Najeriya mazauna ƙasashen waje, tare da ci gaba da neman adalci ta hanyar diflomasiyya da doka.
