Kungiyar Grassroots Mobilisation Network (GMN), daya daga cikin manyan kungiyoyin goyon bayan jam’iyyar African Democratic Congress (ADC), ta yi kakkausar suka ga Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Kasa, Femi Gbajabiamila, kan wasu kalamai da ake zargin ya yi da ke nuna goyon bayan gwamnati ga wasu da aka kora daga jam’iyyar.
A cikin wata sanarwa da Idris Bala Musa ya sanya wa hannu kuma aka fitar a ranar Litinin a Abuja, kungiyar ta zargi Gbajabiamila da nuna cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu zai goyi bayan Bala Nafiu da kuma Hon. Leke Abejide domin su sake samun tasiri a cikin jam’iyyar ADC.
Kungiyar GMN ta bayyana kalaman a matsayin abin damuwa matuka, inda ta bukaci ‘yan Najeriya su kira Shugaban Kasa da ya kare ka’idojin dimokuradiyya, tare da gargadin cewa irin wannan mataki na iya dagula harkokin jam’iyyun adawa.
A cewar kungiyar, an ce Gbajabiamila ya yi wadannan kalamai ne a wajen bikin cika shekaru 20 da aure na Abejide da kuma bikin cikar matarsa shekaru 50, inda aka ruwaito cewa ya ce gwamnatin tarayya za ta taimaka wa Nafiu wajen “kwato jam’iyyarsa”, domin bai wa Abejide damar tsayawa takara a karkashin jam’iyyar ADC.
A baya dai, jam’iyyar ADC ta amince da korar Abejide da Nafiu a babban taronta na kasa bisa zargin aikata ayyukan da suka saba wa dokokin jam’iyya.
Da take mayar da martani, GMN ta ce idan har kalaman gaskiya ne, suna nuna wani “mummunan tsoma baki” a harkokin jam’iyyar adawa, tare da gargadin cewa hakan na iya shafar dimokuradiyyar Najeriya baki daya.
“Yadda wani babban jami’in gwamnati zai fito fili ya ce za a goyi bayan wadanda aka kora daga jam’iyyar adawa, abu ne mai matukar tayar da hankali,” in ji sanarwar.
Kungiyar ta kara da cewa irin wannan dabi’a na iya zama wata hanya ta murkushe muradun jam’iyyun adawa gabanin zabukan 2027.
GMN ta jaddada cewa kowace jam’iyya na da ikon zabar ‘ya’yanta da shugabanninta ba tare da tsoma bakin waje ba, tana mai nuni da Sashe na 40 na Kundin Tsarin Mulkin 1999 da kuma dokokin zabe da ke kare ‘yancin jam’iyyu.
Haka kuma, kungiyar ta bukaci Majalisar Dokoki ta Kasa, kungiyoyin farar hula da kuma kasashen duniya da su sanya ido kan yadda siyasa ke gudana a Najeriya, musamman yayin da ake shirin zabukan 2027.
A karshe, GMN ta bukaci ‘yan Najeriya su kasance masu lura tare da kare dimokuradiyya daga duk wani abu da zai iya raunana ta.
“Ba za a karbe jam’iyyar ADC ta haramtacciyar hanya ba. Dole ne ‘yan Najeriya su tsaya tsayin daka wajen kare dimokuradiyya,” in ji sanarwar.
