Tsohon Mataimakin Gwamnan Babban Bankin Najeriya (CBN), Tunde Lemo, ya janye daga takarar gwamnan jihar Ogun a zaben 2027, inda ya bayyana goyon bayansa ga Sanata Solomon Adeola (Yayi) a matsayin dan takarar jam’iyyar APC na bai ɗaya.
A cikin wata sanarwa da ya fitar a Abeokuta ranar Laraba, Lemo ya ce matakin da ya dauka ya biyo bayan “tsananin tunani da shawarwari masu yawa” da ya yi da shugabannin jam’iyya da masu ruwa da tsaki a jihar.
Ya bayyana cewa wannan ba ja da baya ba ne daga hidimar jama’a, sai dai “dabarar daidaitawa domin amfanin jihar da jam’iyya gaba ɗaya.”
Lemo ya ce shugabannin APC sun yi imanin cewa Adeola zai iya ci gaba da nasarorin gwamnatin yanzu karkashin Gwamna Dapo Abiodun, tare da mayar da Ogun jihar masana’antu da kirkire-kirkire.
Ya kuma yi kira ga magoya bayansa da su mara wa Adeola baya gaba daya, yana mai cewa hadin kai ne zai ba jam’iyyar nasara a zabe mai zuwa.
Wannan mataki na Lemo ya biyo bayan kaddamar da Adeola a matsayin dan takarar gwamna na APC a taron shuwagabannin jam’iyya da aka gudanar a Abeokuta.
