Yayin da ya rage kwanaki 16 a fara Wasannin Commonwealth na 2026 a birnin Glasgow na ƙasar Scotland, tsohon zakaran Commonwealth, Yusuf Alli, ya bukaci ‘yan wasan Team Nigeria su rungumi ladabi, ƙwarewa da jajircewa domin samun nasara a gasar.
Alli ya bayyana hakan ne yayin taron farko na hukuma da aka yi da ‘yan wasan a Aberdeen, Scotland. A matsayinsa na Shugaban Elite Athletes Development and Podium Board, ya ce baiwa kaɗai ba ta isa a samu nasara a manyan gasa, sai an haɗa ta da ladabi da bin ƙa’idoji.
Ya shawarci ‘yan wasan da su kiyaye lokutan cin abinci, horo da zirga-zirgar motar tawaga, tare da tabbatar da samun isasshen hutu domin jiki ya murmure kafin fafatawa.
Ya ce, “Nasara a irin wannan mataki tana farawa ne da ladabi. Ku kasance masu zuwa akan lokaci, ku mutunta jadawalin horo da sauran ƙa’idojin sansani. Idan muka yi ƙananan abubuwa yadda ya kamata, lambobin yabo za su biyo baya.”
Alli ya kuma tunatar da su cewa suna wakiltar Najeriya ne gaba ɗaya, don haka ya dace su nuna ɗabi’a ta gari da haɗin kai a ciki da wajen filin wasa.
“Lokacin da kuka sanya kayan Najeriya, kuna wakiltar miliyoyin ‘yan ƙasa. Ku yi gasa da jarumtaka, ku tallafa wa juna, kuma ku nuna ƙwarewa da mutunci domin a tuna da Team Nigeria ba saboda lambobin yabo kaɗai ba, har ma da kyawawan halaye,” in ji shi.
Yusuf Alli ya taɓa lashe lambar yabo ga Najeriya a Wasannin Commonwealth na 1986, sannan ya lashe zinari a gasar tsalle mai nisa ta maza a shekarar 1990 a Auckland, New Zealand.
Shi ma Mataimakin Shugaban Hukumar Wasannin Guje-guje ta Najeriya (AFN), Akuchukwu Aghazu, ya bukaci ‘yan wasan su kasance masu mayar da hankali, ladabi da haɗin kai har zuwa ƙarshen gasar.
Ya ce haɗin kai zai kasance ɗaya daga cikin manyan makaman Team Nigeria wajen neman nasara a Glasgow.
Ana sa ran Wasannin Commonwealth na 2026 za su gudana ne daga 23 ga Yuli zuwa 2 ga Agusta a birnin Glasgow na ƙasar Scotland.
