Gwamnatin Jihar Abia ta sake jaddada cewa za ta ci gaba da aiwatar da sabbin dokokin da suka shafi baburan haya, tana mai cewa babu wata fa’ida ta tattalin arziki ko siyasa da ta fi kare rayukan al’umma muhimmanci.
Kwamishinan Yaɗa Labarai na jihar, Okey Kanu, ya ce gwamnati ta fahimci cewa dubban mutane na dogaro da sana’ar babur wajen samun abin rayuwa da zirga-zirga, saboda haka ne ta amince da dage ranar fara aiwatar da dokar domin bai wa masu ruwa da tsaki damar cika sabbin sharuddan gwamnati.
Ya bayyana cewa tarar karya dokar za ta kasance Naira 20,000, kuma duk babur da aka ƙwace za a saki ne bayan mai shi ya kammala rajista, tantancewa da sauran ka’idojin da gwamnati ta gindaya.
Kanu ya ce masu amfani da babura na kansu za su ci gaba da zirga-zirga ba tare da matsala ba muddin sun yi rajista da cikakkun takardu, amma ba za su ɗauki fasinjoji ba.
Ya kuma bayyana cewa masu baburan haya za su yi aiki ne kawai a wuraren da gwamnati ta amince da su, kuma dole su sanya rigar shaidar aiki da gwamnati ta tanada.
Haka kuma ya ce duk babura, adaidaita sahu da motocin haya da ke aiki a jihar dole ne su kasance sun yi rajista tare da cika dukkan sharuddan gwamnati.
Kwamishinan ya yi kira ga jama’a da su ba gwamnati haɗin kai, yana mai cewa kare rayuka da dukiyoyin al’umma shi ne babban burin gwamnati.
A bangaren ayyukan raya ƙasa, Kanu ya ce Ma’aikatar Ayyuka ta ƙara ƙaimi wajen gina da gyaran hanyoyi a faɗin jihar.
Ya bayyana cewa tsakanin 16 zuwa 29 ga Yuni, 2026, an gudanar da ayyuka a wurare 14, inda aka kammala ayyuka biyar tare da ƙaddamar da sabon aiki guda ɗaya.
Daga cikin ayyukan da aka kammala akwai titin Obikabia–Umueleke, titin Uzoma–Ohokobe–Afara–Ohokobe, gyaran Chief Nkoro Street zuwa Udeagbala Road a Aba, gyaran Ojari Road da kuma aikin cire datti a Faulks Road.
Ya ƙara da cewa an fara aikin Green Avenue Square a Aba, yayin da ake ci gaba da aikin gina hanyoyi guda 24 a sassa daban-daban na jihar.
A halin da ake ciki, Mai Ba Gwamna Shawara kan Harkokin Tsaro, MacDonald Ubah mai ritaya daga rundunar sojin ruwa, ya bayyana cewa sace ɗalibai biyu a yankin Umuosu Nsulu ya fi kama da safarar yara.
Ya ce bayanai sun nuna cewa yara biyar ne ke cikin wata adaidaita sahu bayan sun tashi daga makaranta, inda aka sauke uku domin su sayo fetur, sannan aka yi awon gaba da sauran biyun.
Ubah ya ce gwamnati na ci gaba da aiki tare da rundunar ‘yan sanda domin ceto yaran, yana mai bayyana cewa an bi wasu bayanan sirri zuwa Ngo-Okpala a Jihar Imo, amma daga baya aka gano bayanan ba su yi daidai ba.
Ya tabbatar da cewa Kwamishinan ‘Yan Sanda na Abia ya tuntubi takwarorinsa a jihohin da ke makwabtaka domin ƙarfafa bincike da ceto yaran.
