Wata kungiya mai suna Political Awareness Coalition (PAC) ta soki kalaman dan majalisar tarayya kuma shugaban marasa rinjaye a majalisar wakilai, Fred Agbedi, kan matsalar tsaro a Najeriya.
A cikin wata sanarwa da shugaban kungiyar, Itodo Vincent, ya sanya wa hannu, PAC ta zargi Agbedi da mayar da matsalar tsaro wata kafa ta siyasa maimakon neman mafita mai dorewa.
Kungiyar ta bayyana cewa ya kamata shugabanni su mayar da hankali wajen gabatar da shawarwari masu amfani da kuma hada kai domin magance matsalolin da ke addabar kasar, maimakon furta kalaman da za su iya haddasa rarrabuwar kawuna.
“Abin takaici ne yadda Hon. Fred Agbedi ya mayar da wata muhimmiyar matsala ta kasa kamar tsaro zuwa batun siyasa. ‘Yan Najeriya na bukatar mafita da hadin kai daga shugabanninsu, ba kalaman siyasa ba,” in ji sanarwar.
PAC ta lura cewa matsalar tsaro ba sabuwa ba ce a Najeriya, domin kasar ta dade tana fama da kalubale irin su ‘yan bindiga, garkuwa da mutane, rikicin makiyaya da manoma, da kuma hare-haren kungiyoyin masu dauke da makamai a sassa daban-daban na kasar.
Kungiyar ta ce warware wadannan matsaloli na bukatar hadin gwiwa tsakanin gwamnati, jami’an tsaro, al’umma da kuma ‘yan siyasa.
Ta kuma bayyana cewa kalaman da Agbedi ya yi na neman shugaban kasa ya yi murabus idan ba a shawo kan matsalar tsaro cikin wata shida ba, ba su dace da matsayinsa na shugaba a majalisa ba.
“A matsayin shugaban marasa rinjaye a majalisar wakilai, bai kamata ya rika fitar da kalaman da suka yi kama da wa’adin siyasa ga shugaban kasa ba. Wannan ba dabi’ar dattijo ba ce,” kungiyar ta bayyana.
PAC ta kara da cewa irin wadannan kalamai suna iya zama wani bangare na shirye-shiryen siyasa gabanin zabukan shekarar 2027 maimakon nuna damuwa ta gaskiya kan halin da al’umma ke ciki.
Kungiyar ta jaddada cewa tsaro nauyi ne na kowa da kowa, don haka bai kamata a mayar da shi filin fafatawar siyasa ba.
Ta kuma jajanta wa iyalan wadanda suka rasa rayukansu ko suka fada hannun masu garkuwa da mutane da sauran nau’o’in tashin hankali a fadin kasar.
A karshe, PAC ta yi kira ga ‘yan adawa da sauran shugabannin siyasa da su gabatar da tsare-tsare da manufofi masu amfani da za su taimaka wajen inganta tsaro da dawo da amincewar jama’a ga gwamnati, maimakon fara yakin neman zabe tun kafin lokaci.
Kungiyar ta kuma sake bayyana goyon bayanta ga kokarin gwamnatin tarayya na magance matsalolin tsaro da farfado da tattalin arzikin kasa.
