Wata babbar kotun tarayya ta bayar da umarnin tsare fitaccen mai fafutukar kare hakkin bil’adama kuma tsohon dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar African Action Congress (AAC), Omoyele Sowore, a gidan gyaran hali na Kuje.
Sowore zai ci gaba da zama a tsare har zuwa ranar 24 ga Yuni, 2026, lokacin da za a ci gaba da sauraron shari’arsa.
Ana tuhumarsa ne da laifuka biyu da suka shafi dokar yaki da laifukan intanet, bayan da Hukumar Tsaron Farin Kaya (DSS) ta zarge shi da yin kalaman batanci da kuma cin zarafin wasu ta hanyar kafafen sadarwa.
Lamarin ya samo asali ne daga wasu sakonni da Sowore ya wallafa a shafukan X da Facebook a watan Agustan 2025, inda ya bayyana Shugaba Bola Ahmed Tinubu a matsayin “mai laifi” dangane da wasu kalamai da aka ce shugaban ya yi yayin wata ziyara zuwa kasar Brazil.
Rahotanni sun ce DSS ta bukaci Sowore ya goge sakonnin, amma ya ki yin hakan, yana mai cewa yana amfani da ‘yancin fadin albarkacin baki ne.
A watan Mayun 2026, Mai Shari’a Mohammed Umar ya yi watsi da bukatar da Sowore ya gabatar na a soke tuhumar da ake masa, bayan kotun ta yanke hukuncin cewa masu gabatar da kara sun gabatar da hujjojin da suka isa a ci gaba da shari’ar.
Bayan umarnin da kotu ta bayar na gudanar da zaman shari’a a kullum, lauyoyin Sowore sun janye daga karar a farkon watan Yuni, lamarin da ya sa ya yanke shawarar kare kansa da kansa.
Sowore ya kuma shigar da bukatar a cire alkalin daga sauraron karar, yana zarginsa da nuna son kai.
Sai dai a ranar 22 ga Yuni, 2026, kotun ta yi watsi da wannan bukata tare da tabbatar da ci gaba da sauraron karar a karkashin alkalin.
Bayan da Sowore bai halarci wani zaman kotu da aka shirya ba, masu gabatar da kara sun zarge shi da kokarin jinkirta shari’ar.
Hakan ya sa kotu ta soke belinsa tare da bayar da sammacin kama shi.
A sakamakon haka, kotun ta bayar da umarnin tsare shi a gidan gyaran hali na Kuje har zuwa ranar da za a ci gaba da sauraron karar.
Gwamnatin tarayya na dogaro da sashe na 24 na sabuwar dokar Cybercrimes Act ta shekarar 2024 wajen gabatar da karar, tana mai cewa kalaman da Sowore ya wallafa karya ne kuma an yi su ne da niyyar tayar da hankalin jama’a.
Sai dai Sowore ya musanta dukkan zarge-zargen da ake masa, yana mai dagewa kan cewa bai aikata wani laifi ba.
Ana sa ran za a ci gaba da sauraron karar a tsakiyar wannan mako yayin da Sowore ke ci gaba da zama a hannun hukuma.
