Tsohon gwamnan Jihar Ekiti, Ayodele Fayose, ya bayyana cewa gwamnan Jihar Oyo, Seyi Makinde, zai fuskanci darasin siyasa kafin babban zaɓen da ke tafe.
Fayose ya bayyana hakan ne yayin wata hira da ya yi a gidan talabijin na Channels Television, inda ya zargi Makinde da rusa tsarin siyasa da kuma karya amincewar abokan siyasa.
Tsohon gwamnan ya yi amfani da wata karin magana wajen bayyana cewa Makinde ya kwace abin da ba nasa ba ne, yana mai gargadin cewa lokaci zai zo da za a mayar da komai zuwa ga masu shi.
A cewarsa, “Za mu koya wa Makinde darasin siyasa. Idan ka girmama ni, za ka samu goyon baya da dukkan darajojina, amma idan ka raina ni, za ka ga wani bangaren na daban. Ni ba dan siyasar da za a dauka da wasa ba ne.”
Fayose ya kuma zargi gwamnan Oyo da raunana jam’iyyar PDP a yankin Kudu maso Yamma tare da kwace masa tsarin siyasa da ya gina tsawon lokaci.
“Makinde ya lalata PDP a Kudu maso Yamma kuma ya karbe tsarin siyasa na. A siyasa ya kamata a rika adalci da mutunta juna,” in ji shi.
Ya kara da cewa dangantakarsa da Makinde ta fara samun matsala ne bayan gwamnan ya nuna aniyarsa ta neman kujerar shugaban kasa.
“Bayyana aniyar takarar shugaban kasa shi ne kuskurensa mafi girma. Yana da damar yin takara, amma bai kamata a ci amanar amana ba. Lokacin zabe ya kusa, kuma za mu gani a gaba,” Fayose ya kara da cewa.
Kalaman Fayose na zuwa ne yayin da ake ci gaba da samun sauye-sauyen siyasa da shirye-shiryen manyan jam’iyyu gabanin zabukan shekarar 2027.
