Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta Najeriya (EFCC) ta fara binciken wani mutum da ke ikirarin kasancewa annabi, Godwin Sunday Ajuluchukwucheya, wanda aka fi sani da Prophet Sunday Koboko, bisa zargin damfarar mabiya cocinsa kudade da suka kai Naira miliyan 70.39.
EFCC ta bayyana hakan ne cikin wata sanarwa da ta wallafa a shafinta na X, inda ta ce jami’anta na shiyyar Enugu suna gudanar da bincike kan zargin da ake yi wa mutumin.
A cewar hukumar, ana zargin ya karbi kudade daga mabiya cocinsa ta hanyoyi daban-daban, ciki har da alkawuran yi musu ayyukan ruhaniya da kuma damar zuba jari domin samun riba.
Daya daga cikin masu shigar da kara, Okey Uwakwe, ya yi zargin cewa mutumin ya karbi Naira miliyan 6.23 daga hannunsa domin gudanar da wasu ayyukan ruhaniya da zai sa dan uwansa da ya dade yana zaune a kasashen waje tun shekarar 1997 ya dawo Najeriya.
Har ila yau, ya yi zargin cewa ya sake karbar Naira miliyan 3.25 domin gudanar da addu’o’i da ayyukan ruhaniya da za su taimaka wa matar dan uwansa ta samu ciki bayan sama da shekaru 15 ba tare da haihuwa ba.
Rahoton EFCC ya nuna cewa wanda ake zargin ya sanar da mabiya cocinsa cewa ya lashe kyautar caca ta Naira biliyan 33, sannan ya bukace su da su bayar da gudunmawar kudi tare da alkawarin za su samu kaso daga kudaden da ya ce ya ci.
Uwakwe ya ce ya kara bayar da Naira miliyan 3.35 cikin wannan tsari, sannan ya sake bayar da Naira 500,000 domin wani kasuwancin sarrafa shinkafa da wanda ake zargin ya bayyana cewa darajarsa ta kai Naira biliyan daya.
A cewarsa, ya biya jimillar Naira miliyan 13.33 amma bai samu wata fa’ida ko riba daga wadannan alkawura ba.
EFCC ta ce yayin gudanar da bincike, wasu mabiya cocin da dama sun fito da makamantan korafe-korafe kan mutumin.
Wasu daga cikinsu sun yi zargin cewa yana sayar musu da kayayyakin da ya kira “Holy Ghost Thunder”, “Miracle Stickers” da kuma “Spiritual Dragons”, yana mai alkawarin cewa za su kawo musu arziki da warware matsalolin rayuwa.
Daya daga cikin wadanda suka ce sun fada tarkonsa ya bayyana cewa ya sayi abin da aka kira “Holy Ghost Thunder” saboda an gaya masa cewa zai magance matsalolinsa, amma bayan biyan kudade babu wani canji da ya samu.
Hukumar EFCC ta ce jimillar kudaden da ake zargin mutumin ya karba daga mabiya cocinsa sun kai Naira miliyan 70.39.
Ta kara da cewa bincike na ci gaba da gudana, kuma za a gurfanar da wanda ake zargin a gaban kotu bayan kammala binciken.
Sai dai EFCC ta jaddada cewa zargin na ci gaba da kasancewa a karkashin bincike, kuma kotu ce kadai ke da ikon tabbatar da laifi ko rashin laifi.
