Kamfanin samar da kayan aikin noma na Agcoms International Trading Limited ya bayyana goyon bayansa ga shirin gwamnatin tarayya na raba taraktoci ga manoma a fadin Najeriya, tare da jaddada cewa horar da masu amfani da kayan aikin da samar da tallafin fasaha na da muhimmanci wajen tabbatar da dorewar nasarar shirin.
Babban jami’in gudanarwa na kamfanin, Okoli Chijioke, ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa inda ya ce samar da injinan noma kadai ba zai wadatar ba idan ba a hada shi da koyar da dabarun amfani da su, gyaransu da kuma samar da ingantattun ayyukan tallafi ba.
A cewarsa, shirin gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na bunkasa amfani da injinan noma wani muhimmin mataki ne da zai taimaka wajen kara yawan amfanin gona da kuma zamanantar da harkokin noma a Najeriya.
Ya ce amfani da kayan aikin noma na zamani na daga cikin hanyoyin da za su kara yawan amfanin gona tare da jawo hankalin matasa zuwa harkar noma.
Chijioke ya bayyana cewa Asusun Bunƙasa Noma na Kasa (NADF) ya rattaba hannu kan yarjejeniyar dala miliyan 70 da kamfanin Agcoms a watan Janairun bana domin samar da taraktoci 2,000 da sauran injinan noma, ciki har da manyan injinan girbi guda 100.
Kamfanin Agcoms, wanda ke da izinin sayar da kayayyakin John Deere a Najeriya kuma abokin hulɗar NADF ne, ya ce yarjejeniyar ta yi daidai da kokarin gwamnatin tarayya na kara samar da abinci a cikin gida.
Sai dai Chijioke ya gargadi cewa taraktoci kadai ba za su magance dukkan kalubalen da ke gaban bangaren noma ba.
Ya ce nasarar shirin za ta dogara ne kan samar da horo ga masu amfani da injinan, hanyoyin gyara su, tallafin kudi da kuma ingantattun ayyukan bayan saye domin tabbatar da cewa kayan aikin na ci gaba da aiki yadda ya kamata.
Kamfanin ya kuma bayyana cewa shirin ya kunshi hada wasu daga cikin injinan a cikin Najeriya, matakin da ake sa ran zai taimaka wajen koyar da sabbin dabaru, samar da ayyukan yi da kuma bunkasa fasahar kere-keren injinan noma a kasar.
A cewar kamfanin, samar da horo ga masu amfani da injinan, ayyukan gyare-gyare da kuma tallafin bayan saye na daga cikin muhimman matakan da za su tabbatar da cewa manoma sun samu cikakkiyar fa’ida daga kayan aikin.
Chijioke ya tuna cewa Shugaba Tinubu ne ya fara bayyana wannan shiri a jawabinsa na ranar samun ‘yancin kai a watan Oktoban 2024, lokacin da Majalisar Zartarwa ta Tarayya ta amince da kafa masana’antar hada taraktocin John Deere da sauran kayan aikin noma a Najeriya.
Tun daga wannan lokaci, jami’an gwamnati ke bayyana shirin a matsayin daya daga cikin manyan nasarorin gwamnatin Tinubu a bangaren noma.
Kamfanin Agcoms ya sake tabbatar da kudurinsa na ci gaba da tallafawa shirin gwamnati ta hanyar samar da kayan aiki, kwarewar fasaha, kayan gyara da kuma ayyukan da za su taimaka wajen inganta noma da kara yawan amfanin gona.
Ya kara da cewa dorewar amfani da injinan noma na bukatar tsari mai dorewa wanda zai hada samar da kayan aiki, horaswa, tallafin fasaha da kuma tsarin gyara mai inganci domin tabbatar da cewa jarin da aka zuba na ci gaba da amfani ga manoma da al’ummomin karkara.
