Hukumar Kwastam ta Najeriya, shiyyar ayyuka ta musamman ta Zone A da ke Legas, ta samu gagarumar nasara bayan kwace hauren giwa guda 22 da darajarsu ta kai Naira miliyan 126.39 a kasuwar bayan-fage ta duniya.
An gudanar da samamen ne tare da hadin gwiwar Hukumar Kula da Muhalli ta Kasa (NESREA) da kuma kungiyar yaki da safarar namun daji ta Wildlife Justice Commission (WJC), inda aka kama mutane hudu da ake zargi da hannu a safarar hauren giwa ba bisa ka’ida ba.
Rahotanni sun nuna cewa jami’an tsaro sun kwace hauren giwar masu nauyin kilogram 130.84 a yankin Ofada da ke Mowe a Jihar Ogun, yayin da aka kama sauran wadanda ake zargi a wurare daban-daban na Jihar Legas.
Kwamandan Kwastam na Zone A, Gambo Aliyu, ya bayyana cewa nasarar ta nuna irin kudirin hukumar na dakile safarar namun daji da kuma kare dabbobin da ke fuskantar barazanar bacewa.
Ya ce Najeriya tana cikin kasashen da suka rattaba hannu kan yarjejeniyar CITES wadda ke hana safarar dabbobi da tsirrai masu hadarin bacewa, yana mai gargadin masu aikata irin wadannan laifuka da su guji amfani da Najeriya a matsayin hanyar safarar kayan haramtattu.
Aliyu ya kuma yaba da hadin gwiwar NESREA da WJC, yana mai cewa bayanan sirri da goyon bayan da suka bayar ne suka taimaka wajen samun wannan nasara.
Hukumar ta ce har yanzu ana ci gaba da bincike kan lamarin, yayin da ake tsare da wadanda ake zargi tare da motar da aka yi amfani da ita wajen safarar hauren giwar domin gurfanar da su a gaban kotu bayan kammala bincike.
