Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, a ranar Litinin ya bayyana a gaban Babbar Kotun Jihar Kaduna yayin da shari’ar da Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa (ICPC) ta shigar a kansa ta ci gaba.
Bidiyon da tashar ARISE NEWS ta wallafa ya nuna El-Rufai sanye da babban riga (Agbada), yana ratsawa cikin cunkoson jama’a a harabar kotu, inda magoya baya, lauyoyi da sauran jama’a suka taru.
Kafin shiga kotu, an ji shi yana tattaunawa da wani abokin tafiya game da taron ƙasa na jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) da aka shirya gudanarwa a ranar Talata.
“Gobe kenan taron mu, ko?” in ji El-Rufai.
“Da yardar Allah (Insha Allah),” abokin nasa ya amsa.
Wannan tattaunawa na nuna cewa El-Rufai na ci gaba da harkokin siyasa duk da shari’ar da ke gudana a kansa.
A halin yanzu, yana fuskantar tuhuma tare da Amadu Sule kan zarge-zarge da suka haɗa da almundahana, amfani da madafun iko ba bisa ƙa’ida ba, da kuma bayar da fa’ida ba tare da halalci ba.
A wata shari’a daban a Babbar Kotun Tarayya da ke Kaduna, hukumar ICPC ta kuma gurfanar da shi kan ƙarin tuhume-tuhume 10 da suka shafi zargin almundahana da kuma halatta kuɗaɗen haramtacciyar hanya, wanda ya kai kimanin ₦579.6 miliyan da kuma $1.1 miliyan.
El-Rufai dai ya sha nanata cewa ba shi da laifi a dukkan tuhumar da ake yi masa.
Rahotanni sun nuna cewa tun bayan dawowarsa daga Alkahira, Masar a ranar 12 ga Fabrairu, 2026, yake ci gaba da fuskantar shari’o’i a kotu. An fara tsare shi a hannun hukumar EFCC kafin daga bisani ICPC ta karɓe shi.
Kotun Tarayya da ke Kaduna ta saka ranar 14 ga Afrilu domin sauraron buƙatar belinsa, wacce ta zo daidai da ranar taron ADC na ƙasa, lamarin da ya ƙara jawo cece-kuce a fagen siyasa.
Jam’iyyar ADC kuma ta yi zargin cewa ana amfani da tsarin shari’a wajen yi masa katsalandan na siyasa.
