Fitacciyar jarumar fina-finan Najeriya, Toyin Abraham, ta mayar da martani kan suka da ake yi mata dangane da dabi’arta ta durƙusawa wajen gaishe da manya a wuraren taro.
Jarumar ta bayyana cewa ba za ta daina wannan al’ada ba, musamman ga mutanen da take ganin sun cancanci girmamawa.
Toyin Abraham ta bayyana hakan ne a shafinta na X a ranar Asabar, yayin da take mayar da martani ga wata mabiyarta mai suna Lady Victoria, wacce ta bukace ta da ta daina abin da ta kira “durƙusawar banza,” tana mai cewa hakan na iya jawo rashin daraja.
A martaninta, Abraham ta ce:
“Ba zan daina durƙusawa ga mutanen da suke da daraja a wurina ba, masoyiyata. Zan ci gaba da durƙusawa da gwiwoyina biyu wajen gaishe da mutanen da suka cancanci hakan, ko da matsayinsu ya kasance.”
Wannan muhawara ta samo asali ne bayan wani bidiyo daga bikin cikar shekaru 70 na tsohon gwamnan jihar Ogun, Gbenga Daniel, inda aka ga jarumar tana durƙusawa gaban fitacciyar ‘yar kasuwa, Shade Okoya, da mijinta Rasaq Okoya, tare da sauran manyan baki.
Sai dai Lady Victoria ta nuna damuwa cewa wasu daga cikin matan da Abraham ke durƙusawa musu ba su fi ta tsufa sosai ba, tana mai cewa hakan na iya sa ta raina kanta a idon jama’a.
Duk da haka, Toyin Abraham ta jaddada cewa wannan dabi’a ta girmamawa wani bangare ne na tarbiyyarta, kuma ba za ta daina ba saboda ra’ayin wasu mutane.
