Gwamnatin tarayya ta kaddamar da wani sabon shiri na bayar da agajin gaggawa ga marasa lafiya a jihar Kano, wanda ya fara da amincewar Asibitin Kashi na Dala, dake Kano, karkashin hukumar bada agajin gaggawa ta kasa (NEMSAS).
Da yake jawabi yayin bikin kaddamar da shirin ranar Juma’a a asibitin, babban daraktan kula da lafiya, Dakta Nurudeen Isa, ya ce shirin ya nuna wani babban ci gaba a fannin kiwon lafiya ga gwamnati mai ci, da nufin bayar da kulawa ga marasa galihu.
“A yau, mun gayyace ku da ku baje kolin daya daga cikin muhimman abubuwan kiwon lafiya na wannan gwamnati na bayar da kulawar gaggawa ga duk marasa lafiya da aka kawo daga kowane yanki na wannan jiha zuwa wannan asibiti, inda zai su sami kulawar lafiya kyauta cikin sa’o’i 48 na farko,” in ji Dakta Isa.
Ya bayyana cewa, NEMSAS, wata kafa da gwamnatin tarayya ta samar da kudaden da ake samu kai tsaye daga asusun tarayya, an tsara shi ne domin tabbatar da cewa dukkan ‘yan Nijeriya, musamman ma marasa galihu, sun sami damar samun kulawar ceton rai a cikin gaggawa.
SolaceBase ta ruwaito cewa shirin ya kunshi majinyata da suka hadu da hadurran ababen hawa, da gaugawar haihuwa, saran maciji, harbin bindiga, da sauran munanan yanayi.
Wannan shi ne wuri na farko a jihar Kano da aka amince da shi a karkashin wannan shirin. Sauran, da suka hada da asibitocin gwamnatin jihar, nan ba da jimawa ba za a yi musu rajista,” ya kara da cewa, shirin zai iya ceton rayuka da kuma hana afkuwar rikice-rikice a lokutan gaggawa.
Shima da yake jawabi a wajen taron, Dakta Emuren Doubra, shugaban aiyuka na NEMSAS, wanda ya wakilci Dr. Said Ahmed Dumbulwa, Darakta/ Manajan Shirye-shiryen NEMSAS daga Ma’aikatar Lafiya ta tarayya, ya tabbatar da dorewar shirin, wanda ke samun goyon bayan tallafin da doka ta tanada daga asusun kula da lafiya na kasa da ke tushen tsarin kiwon lafiya na kasa.
“Daga wannan asusun, an ware kashi 5% na musamman don kula da lafiyar gaggawa. Muna hada kai da masu zaman kansu da kuma cibiyoyin kiwon lafiya na jama’a don tabbatar da cewa ba a bar ‘yan Najeriya matalauta da marasa galihu su dauki nauyin kulawar gaggawa,” in ji Doubra.
A wani bangare na aiwatar da shirin, shirin ya hada da tawagar motocin daukar marasa lafiya sanye da kayan aikin jinya da ma’aikata, tare da hadin gwiwar hukumar kiyaye hadurra ta kasa (FRSC), domin jigilar wadanda hadarin ya rutsa da su da sauran majinyatan gaggawa daga kowane wuri a cikin jihar Kano zuwa asibiti.
Wadannan motocin daukar marasa lafiya ba na sufuri ba ne kawai. Suna ba da kulawar gaggawa tun daga wurin da lamarin ya faru kuma suna sanar da asibitin tukuna don a yi shirye-shiryen karbar mara lafiyar,” Dr. Dumbulwa ya bayyana.
Wani majinyaci da ya ci gajiyar shirin, Aliyu Abdul, ya bayyana cewa a baya an gaya masa a asibitocin Enugu da Legas cewa za a yanke kafar sa sakamakon wani mummunan hatsari da ya faru.
“Lokacin da na yi hatsari, an gaya mini cewa za a yanke kafata, amma da na zo nan, na sami ingantaccen magani.
“Yanzu na murmure – kun ga ina tsaye,” in ji shi, yana nuna godiya ga sa’o’i 48 na jinya kyauta.
Ana sa ran shirin zai fadada zuwa wasu asibitoci a fadin jihar Kano tare da zama abin koyi wajen bayar da agajin gaggawa a fadin kasar.
