Close Menu
  • Home
  • News
    • National
    • International
  • Asrah 24 TV
  • Education
  • Health
  • Podcast
  • Politics
  • Sports
  • More
    • Agriculture
    • Business
    • Climate Changes
    • Culture
    • Environment
    • Entertainment
    • Opinion
    • Religious
    • Security
    • Videos
Facebook X (Twitter) YouTube WhatsApp Telegram
Facebook X (Twitter) WhatsApp Telegram
ASRAH 24 MEDIA
Subscribe
  • Home
  • News
    1. National
    2. International
    3. View All

    Najeriya Ta Kai Dala $18.4 Biliyan a Cinikayyar Cikin Afirka a 2024

    June 28, 2025

    Afreximbank Ta Ba Najeriya Tallafin $50 Biliyan Don Manyan Ayyuka

    June 28, 2025

    Mutane 28 sun mutu sakamakon gudun wuce sa’a a jihar Ondo- FRSC

    February 2, 2025

    Najeriya Ta Fuskanci Limit na Visa zuwa Amurka – 3 Mako Kaɗai!

    July 9, 2025

    Gwamnatin Tarayya Tare da Faransa Za Su Inganta ICT a Jami’o’in Najeriya da Tallafin Naira Biliyan 38

    July 4, 2025

    Zafin Rana Mai Tsanani Ya Ɓarke a Turai: Matsalar Heat Dome

    June 30, 2025

    Najeriya Ta Samu Jarin Waje Har Dala Biliyan 2.5 Daga Masarautar Saudiyya

    June 29, 2025

    Tiwa Savage Ta Bayyana Yadda Take Rashin Kulawar Don Jazzy Da Mavin

    May 20, 2026

    NERC Da ONSA Sun Hada Kai Don Dakile Lalata Kayan Wutar Lantarki

    May 20, 2026

    Iran Ta Shirya Auren Jama’a Ga Masu Shirin Sadaukar Da Rayukansu A Yaki

    May 19, 2026

    NUJ-FCT Ta Gargadi ‘Yan Jarida Kan Yada Labaran Karya Gabanin Zabuka

    May 19, 2026
  • Asrah 24 TV
  • Education

    Sojojin Najeriya Sun Yaye Sabbin Paratroopers Bayan Kammala Horon Tsalle Daga Jirgin Sama

    June 5, 2026

    Achievers University Ta Bankado Zargin Damfarar Kudin Makaranta Ta N457.5m

    May 25, 2026

    NYSC ta shawarci iyaye su taimaka wa ‘ya’yansu da karin kudin tafiya

    May 21, 2026

    NYSC ta tsawaita wa wasu masu bautar kasa hidima a Gombe

    May 21, 2026

    Najeriya da Italiya sun hada kai domin tara dala biliyan 5 don tallafa wa ilimi

    May 21, 2026
  • Health

    OYO TA KWANTAR WA MAZAUNA HANKALI KAN CUTAR EBOLA, TA SA MA’AIKATAN LAFIYA CIKIN SHIRI

    June 4, 2026

    Likitan Ondo Sun Ƙara Matsin Lamba Kan Gwamnati, Sun Yi Barazanar Tsunduma Yajin Aiki

    May 19, 2026

    Coroner’s Court ta dakatar da shari’ar mutuwar ɗan Chimamanda Adichie har sai umarnin Attorney-General

    May 5, 2026

    Sarki Charles III Ya Yarda Cewa Ciwon Kansar Da Ke Damunsa Na Iya Hana Shi Ganin Dogon Aikin Da Ya Kafa

    April 30, 2026

    Masana lafiya sun bukaci daukar matakin gaggawa kan cutar sickle cell a Najeriya da Afirka

    April 29, 2026
  • Podcast
  • Politics

    Tinubu Torchbearers Zai Taimaka Wajen Wayar Da Kai Da Tallafawa Gwamnati — APC Women Leader

    June 4, 2026

    INEC Ta Shirya Tsaf Domin Zaben Sanatan Ondo Kudu Ranar 20 ga Yuni

    June 4, 2026

    LP Ta Kammala Zaben Fidda Gwani, Ta Tsayar da ‘Yan Takara na Majalisa a Anambra

    June 4, 2026

    Peter Obi Ya Kare Adeboye, Ya Gargadi Matasa Kan Rarrabuwar Kabilanci Da Addini

    June 4, 2026

    Tsohon Firaministan Senegal Ousmane Sonko Ya Zama Kakakin Majalisa

    May 26, 2026
  • Sports

    Shaibu Ya Yabawa Super Eagles Da Adeboye Kan Nasarorin Unity Cup Da Wasan Poland

    June 4, 2026

    Super Eagles Na Da Ƙarfin Doke Kowace Ƙasa Duk Da Rashin Tikitin Gasar Kofin Duniya

    June 4, 2026

    Kai Havertz Ya Yabawa Jamus Karfin ‘Yan Hari Gaban Gasar Kofin Duniya Ta 2026

    June 4, 2026

    Marinakis Ya Yi Rikici A Athens Yayin Gasar EuroLeague

    May 25, 2026

    Spurs Sun Farfado Thunder, Wembanyama Ya Jagoranci Nasara A Wasan NBA

    May 25, 2026
  • More
    • Agriculture
    • Business
    • Climate Changes
    • Culture
    • Environment
    • Entertainment
    • Opinion
    • Religious
    • Security
    • Videos
ASRAH 24 MEDIA
Home » Gwamnatin Najeriya za ta fara bada agajin gaggawa kyauta ga marasa Lafiya a Kano
Health

Gwamnatin Najeriya za ta fara bada agajin gaggawa kyauta ga marasa Lafiya a Kano

Asrah24 MediaBy Asrah24 MediaMay 17, 20253 Mins Read
Facebook Twitter WhatsApp
polish save

Gwamnatin tarayya ta kaddamar da wani sabon shiri na bayar da agajin gaggawa ga marasa lafiya a jihar Kano, wanda ya fara da amincewar Asibitin Kashi na Dala, dake Kano, karkashin hukumar bada agajin gaggawa ta kasa (NEMSAS).

Da yake jawabi yayin bikin kaddamar da shirin ranar Juma’a a asibitin, babban daraktan kula da lafiya, Dakta Nurudeen Isa, ya ce shirin ya nuna wani babban ci gaba a fannin kiwon lafiya ga gwamnati mai ci, da nufin bayar da kulawa ga marasa galihu.

“A yau, mun gayyace ku da ku baje kolin daya daga cikin muhimman abubuwan kiwon lafiya na wannan gwamnati na bayar da kulawar gaggawa ga duk marasa lafiya da aka kawo daga kowane yanki na wannan jiha zuwa wannan asibiti, inda zai su sami kulawar lafiya kyauta cikin sa’o’i 48 na farko,” in ji Dakta Isa.

Ya bayyana cewa, NEMSAS, wata kafa da gwamnatin tarayya ta samar da kudaden da ake samu kai tsaye daga asusun tarayya, an tsara shi ne domin tabbatar da cewa dukkan ‘yan Nijeriya, musamman ma marasa galihu, sun sami damar samun kulawar ceton rai a cikin gaggawa.

SolaceBase ta ruwaito cewa shirin ya kunshi majinyata da suka hadu da hadurran ababen hawa, da gaugawar haihuwa, saran maciji, harbin bindiga, da sauran munanan yanayi.

Wannan shi ne wuri na farko a jihar Kano da aka amince da shi a karkashin wannan shirin. Sauran, da suka hada da asibitocin gwamnatin jihar, nan ba da jimawa ba za a yi musu rajista,” ya kara da cewa, shirin zai iya ceton rayuka da kuma hana afkuwar rikice-rikice a lokutan gaggawa.

Shima da yake jawabi a wajen taron, Dakta Emuren Doubra, shugaban aiyuka na NEMSAS, wanda ya wakilci Dr. Said Ahmed Dumbulwa, Darakta/ Manajan Shirye-shiryen NEMSAS daga Ma’aikatar Lafiya ta tarayya, ya tabbatar da dorewar shirin, wanda ke samun goyon bayan tallafin da doka ta tanada daga asusun kula da lafiya na kasa da ke tushen tsarin kiwon lafiya na kasa.

“Daga wannan asusun, an ware kashi 5% na musamman don kula da lafiyar gaggawa. Muna hada kai da masu zaman kansu da kuma cibiyoyin kiwon lafiya na jama’a don tabbatar da cewa ba a bar ‘yan Najeriya matalauta da marasa galihu su dauki nauyin kulawar gaggawa,” in ji Doubra.

A wani bangare na aiwatar da shirin, shirin ya hada da tawagar motocin daukar marasa lafiya sanye da kayan aikin jinya da ma’aikata, tare da hadin gwiwar hukumar kiyaye hadurra ta kasa (FRSC), domin jigilar wadanda hadarin ya rutsa da su da sauran majinyatan gaggawa daga kowane wuri a cikin jihar Kano zuwa asibiti.

Wadannan motocin daukar marasa lafiya ba na sufuri ba ne kawai. Suna ba da kulawar gaggawa tun daga wurin da lamarin ya faru kuma suna sanar da asibitin tukuna don a yi shirye-shiryen karbar mara lafiyar,” Dr. Dumbulwa ya bayyana.

Wani majinyaci da ya ci gajiyar shirin, Aliyu Abdul, ya bayyana cewa a baya an gaya masa a asibitocin Enugu da Legas cewa za a yanke kafar sa sakamakon wani mummunan hatsari da ya faru.

“Lokacin da na yi hatsari, an gaya mini cewa za a yanke kafata, amma da na zo nan, na sami ingantaccen magani.

“Yanzu na murmure – kun ga ina tsaye,” in ji shi, yana nuna godiya ga sa’o’i 48 na jinya kyauta.

Ana sa ran shirin zai fadada zuwa wasu asibitoci a fadin jihar Kano tare da zama abin koyi wajen bayar da agajin gaggawa a fadin kasar.

Share. Facebook Twitter Telegram WhatsApp
Previous ArticleMajalisar Dokokin jihar Kano tace Hukumar KAROTA batada Hurumun Kama masu karya dokokin titi a jihar Kano
Next Article Zamu ci gaba da karya farashin kayan abinci a Najeriya: BUA

Related Posts

OYO TA KWANTAR WA MAZAUNA HANKALI KAN CUTAR EBOLA, TA SA MA’AIKATAN LAFIYA CIKIN SHIRI

June 4, 2026

Likitan Ondo Sun Ƙara Matsin Lamba Kan Gwamnati, Sun Yi Barazanar Tsunduma Yajin Aiki

May 19, 2026

Coroner’s Court ta dakatar da shari’ar mutuwar ɗan Chimamanda Adichie har sai umarnin Attorney-General

May 5, 2026

Sarki Charles III Ya Yarda Cewa Ciwon Kansar Da Ke Damunsa Na Iya Hana Shi Ganin Dogon Aikin Da Ya Kafa

April 30, 2026
Add A Comment
Leave A Reply Cancel Reply

Latest Posts

Mummunar Hanyar Kauye Na Hana Yara Zuwa Makaranta A Akwa Ibom — Mazauna Yanki

June 5, 2026

Sojojin Najeriya Sun Yaye Sabbin Paratroopers Bayan Kammala Horon Tsalle Daga Jirgin Sama

June 5, 2026

Dayo Amusa Ta Soki Matsin Lambar Da Ake Yi Wa Fitattun Jarumai Kan Matsalolin Kasa

June 5, 2026

Kungiya Ta Bukaci Hadin Kan ‘Yan Najeriya Wajen Yaki Da Matsalar Tsaro

June 5, 2026

TCN Ta Sanar da Katse Wutar Lantarki a Sassan Delta Saboda Ayyukan Gyaran Tashar Wuta

June 5, 2026
Connect with us
  • Facebook
  • Twitter
  • YouTube
  • WhatsApp
  • Instagram
  • TikTok
Top Posts
Advertisement
© 2026 ASRAH 24 MEDIA. Developed by ENGRMKS & CO..
  • Home
  • About Us
  • Contact Us
  • Privacy Policy

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.