Close Menu
  • Home
  • News
    • National
    • International
  • Asrah 24 TV
  • Education
  • Health
  • Podcast
  • Politics
  • Sports
  • More
    • Agriculture
    • Business
    • Climate Changes
    • Culture
    • Environment
    • Entertainment
    • Opinion
    • Religious
    • Security
    • Videos
Facebook X (Twitter) YouTube WhatsApp Telegram
Facebook X (Twitter) WhatsApp Telegram
ASRAH 24 MEDIA
Subscribe
  • Home
  • News
    1. National
    2. International
    3. View All

    CBN Ta Ce Sauye-Sauyen Tattalin Arziki Sun Kafa Tubalin Ci Gaba Da Daidaiton Arzikin Najeriya

    August 6, 2026

    KOTU TA SAMU MACE DA LAIFIN YUNKURIN KASHE ƳAR SHEKARA 9 BAYAN TA YAUDARE TA ZUWA DAJI

    June 26, 2026

    KOTU TA KI SAKIN SOWORE, TA DAGE YANKE HUKUNCI ZUWA 30 GA YUNI

    June 24, 2026

    Sarkin Ilorin Ya Taya Musulmi Murnar Sabuwar Shekarar Hijira, Ya Yi Kiran Hadin Kai

    June 16, 2026

    📰 Labarin Yanar Gizo (Hausa Version): Kaduna Pilgrims Board Ya Tabbatar An Yi Hadaya Ga Duk Masu Biyan Kuɗi

    June 9, 2026

    Najeriya Ta Fuskanci Limit na Visa zuwa Amurka – 3 Mako Kaɗai!

    July 9, 2025

    Gwamnatin Tarayya Tare da Faransa Za Su Inganta ICT a Jami’o’in Najeriya da Tallafin Naira Biliyan 38

    July 4, 2025

    Zafin Rana Mai Tsanani Ya Ɓarke a Turai: Matsalar Heat Dome

    June 30, 2025

    CBN Ta Ce Sauye-Sauyen Tattalin Arziki Sun Kafa Tubalin Ci Gaba Da Daidaiton Arzikin Najeriya

    August 6, 2026

    Trump Ya Bukaci Kamfanonin Mai Su Rage Farashin Mai Bayan Zargin Samun Ribar Da Ta Yi Yawa

    August 5, 2026

    Hukumar Shige Da Fice Ta Tabbatar Da Cewa Ba A Dakatar Da Ayyukan Fitar Da Fasfo Ba

    August 5, 2026

    Yadda Sha’awar Mahaifiyata Ta Sa Na Zama Mai Binciken Abinci – Opeyemi Famakin

    August 4, 2026
  • Asrah 24 TV
  • Education

    Farfesa Oloyede Ya Ajiye Muƙaminsa a JAMB Bayan Shekaru 10, Ya Koma Koyarwa

    July 31, 2026

    Ɗalibin UNILAG Ya Lashe Gasar Huawei ta ICT ta Duniya a China

    July 31, 2026

    Yajin Aikin ASUU Ya Jefa Daliban Jami’ar AAUA Cikin Rashin Tabbas

    July 27, 2026

    Save the Children Ta Mara Wa Kaduna Baya Don Mayar Da Yara 100,000 Makaranta

    July 24, 2026

    ‘Yar Ministan Abuja Nyesom Wike Ta Samu Digirin Lauya A Birtaniya

    July 22, 2026
  • Health

    ICPC Ta Gurfanar da Likitan El-Rufai Kan Zargin Ƙirƙirar Rahoton Lafiya na Karya Domin Neman Beli

    July 20, 2026

    Masana Sun Yi Gargadin Cewa Gano Cutar Sarcoma Da Wuri Na Iya Taimakawa Wajen Ceto Rayuka

    July 16, 2026

    Kusan Kashi 45% Na Cutar Dementia Ana Iya Hana Ta Ta Hanyar Canza Salon Rayuwa

    July 15, 2026

    Yobe, Qatar Charity Sun Kaddamar da Shirin Kyauta na Duba Ido da Aikin Cataract

    July 15, 2026

    Shahararren Mai Binciken Abinci, Opeyemi Famakin, Ya Ba Da Labarin Yadda Aikin 9-zuwa-5 Ya Gina Rayuwarsa

    July 13, 2026
  • Podcast
  • Politics

    Uzodimma Ya Mayar Wa Davido Martani Kan Zaɓen Gwamnan Osun

    August 6, 2026

    Zaɓen 15 Ga Agusta Zai Isar Da Saƙo Ga APC – Gwamna Adeleke

    August 6, 2026

    Gwamnatin Tarayya Za Ta Gina Hasumiyoyin Sadarwa 3,700 Domin Haɗa Fiye Da Mutane Miliyan 20 Da Intanet

    August 5, 2026

    Gwamnatin Osun Ta Sake Raba Tallafin Kuɗi Ga Ma’aikatan Jiha

    August 5, 2026

    Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Kalubalantar Wasu Tanade-Tanaden Dokar Zaɓe Ta 2026

    August 4, 2026
  • Sports

    NANS Ta Bukaci ‘Yan Arewa Su Guji Siyasantar Da Gyaran Tsarin Fitar Da Fasfo

    August 6, 2026

    Usyk Ya Bayyana Dangantakarsa Da Anthony Joshua, Ya Goyi Bayan Nasararsa Kan Tyson Fury

    August 2, 2026

    Portable Ya Sha Kaye A Hannun Charles Okocha A Fafatawar Dambe Ta Sake

    August 2, 2026

    Super Falcons Sun Doke Zambia Da Ɗan Wasa 10, Oshoala Ta Kai Najeriya Ga Nasara

    August 2, 2026

    Najeriya Ta Kafa Sabon Tarihi, Ta Kai Wasu Ƴan Wasa Zagayen Ƙarshe

    July 31, 2026
  • More
    • Agriculture
    • Business
    • Climate Changes
    • Culture
    • Environment
    • Entertainment
    • Opinion
    • Religious
    • Security
    • Videos
ASRAH 24 MEDIA
Home » Gwamnatin Najeriya za ta fara bada agajin gaggawa kyauta ga marasa Lafiya a Kano
Health

Gwamnatin Najeriya za ta fara bada agajin gaggawa kyauta ga marasa Lafiya a Kano

Asrah24 MediaBy Asrah24 MediaMay 17, 20253 Mins Read
Facebook Twitter WhatsApp
polish save

Gwamnatin tarayya ta kaddamar da wani sabon shiri na bayar da agajin gaggawa ga marasa lafiya a jihar Kano, wanda ya fara da amincewar Asibitin Kashi na Dala, dake Kano, karkashin hukumar bada agajin gaggawa ta kasa (NEMSAS).

Da yake jawabi yayin bikin kaddamar da shirin ranar Juma’a a asibitin, babban daraktan kula da lafiya, Dakta Nurudeen Isa, ya ce shirin ya nuna wani babban ci gaba a fannin kiwon lafiya ga gwamnati mai ci, da nufin bayar da kulawa ga marasa galihu.

“A yau, mun gayyace ku da ku baje kolin daya daga cikin muhimman abubuwan kiwon lafiya na wannan gwamnati na bayar da kulawar gaggawa ga duk marasa lafiya da aka kawo daga kowane yanki na wannan jiha zuwa wannan asibiti, inda zai su sami kulawar lafiya kyauta cikin sa’o’i 48 na farko,” in ji Dakta Isa.

Ya bayyana cewa, NEMSAS, wata kafa da gwamnatin tarayya ta samar da kudaden da ake samu kai tsaye daga asusun tarayya, an tsara shi ne domin tabbatar da cewa dukkan ‘yan Nijeriya, musamman ma marasa galihu, sun sami damar samun kulawar ceton rai a cikin gaggawa.

SolaceBase ta ruwaito cewa shirin ya kunshi majinyata da suka hadu da hadurran ababen hawa, da gaugawar haihuwa, saran maciji, harbin bindiga, da sauran munanan yanayi.

Wannan shi ne wuri na farko a jihar Kano da aka amince da shi a karkashin wannan shirin. Sauran, da suka hada da asibitocin gwamnatin jihar, nan ba da jimawa ba za a yi musu rajista,” ya kara da cewa, shirin zai iya ceton rayuka da kuma hana afkuwar rikice-rikice a lokutan gaggawa.

Shima da yake jawabi a wajen taron, Dakta Emuren Doubra, shugaban aiyuka na NEMSAS, wanda ya wakilci Dr. Said Ahmed Dumbulwa, Darakta/ Manajan Shirye-shiryen NEMSAS daga Ma’aikatar Lafiya ta tarayya, ya tabbatar da dorewar shirin, wanda ke samun goyon bayan tallafin da doka ta tanada daga asusun kula da lafiya na kasa da ke tushen tsarin kiwon lafiya na kasa.

“Daga wannan asusun, an ware kashi 5% na musamman don kula da lafiyar gaggawa. Muna hada kai da masu zaman kansu da kuma cibiyoyin kiwon lafiya na jama’a don tabbatar da cewa ba a bar ‘yan Najeriya matalauta da marasa galihu su dauki nauyin kulawar gaggawa,” in ji Doubra.

A wani bangare na aiwatar da shirin, shirin ya hada da tawagar motocin daukar marasa lafiya sanye da kayan aikin jinya da ma’aikata, tare da hadin gwiwar hukumar kiyaye hadurra ta kasa (FRSC), domin jigilar wadanda hadarin ya rutsa da su da sauran majinyatan gaggawa daga kowane wuri a cikin jihar Kano zuwa asibiti.

Wadannan motocin daukar marasa lafiya ba na sufuri ba ne kawai. Suna ba da kulawar gaggawa tun daga wurin da lamarin ya faru kuma suna sanar da asibitin tukuna don a yi shirye-shiryen karbar mara lafiyar,” Dr. Dumbulwa ya bayyana.

Wani majinyaci da ya ci gajiyar shirin, Aliyu Abdul, ya bayyana cewa a baya an gaya masa a asibitocin Enugu da Legas cewa za a yanke kafar sa sakamakon wani mummunan hatsari da ya faru.

“Lokacin da na yi hatsari, an gaya mini cewa za a yanke kafata, amma da na zo nan, na sami ingantaccen magani.

“Yanzu na murmure – kun ga ina tsaye,” in ji shi, yana nuna godiya ga sa’o’i 48 na jinya kyauta.

Ana sa ran shirin zai fadada zuwa wasu asibitoci a fadin jihar Kano tare da zama abin koyi wajen bayar da agajin gaggawa a fadin kasar.

Share. Facebook Twitter Telegram WhatsApp
Previous ArticleMajalisar Dokokin jihar Kano tace Hukumar KAROTA batada Hurumun Kama masu karya dokokin titi a jihar Kano
Next Article Zamu ci gaba da karya farashin kayan abinci a Najeriya: BUA

Related Posts

ICPC Ta Gurfanar da Likitan El-Rufai Kan Zargin Ƙirƙirar Rahoton Lafiya na Karya Domin Neman Beli

July 20, 2026

Masana Sun Yi Gargadin Cewa Gano Cutar Sarcoma Da Wuri Na Iya Taimakawa Wajen Ceto Rayuka

July 16, 2026

Kusan Kashi 45% Na Cutar Dementia Ana Iya Hana Ta Ta Hanyar Canza Salon Rayuwa

July 15, 2026

Yobe, Qatar Charity Sun Kaddamar da Shirin Kyauta na Duba Ido da Aikin Cataract

July 15, 2026
Add A Comment
Leave A Reply Cancel Reply

Latest Posts

Uzodimma Ya Mayar Wa Davido Martani Kan Zaɓen Gwamnan Osun

August 6, 2026

CBN Ta Ce Sauye-Sauyen Tattalin Arziki Sun Kafa Tubalin Ci Gaba Da Daidaiton Arzikin Najeriya

August 6, 2026

Zaɓen 15 Ga Agusta Zai Isar Da Saƙo Ga APC – Gwamna Adeleke

August 6, 2026

NANS Ta Bukaci ‘Yan Arewa Su Guji Siyasantar Da Gyaran Tsarin Fitar Da Fasfo

August 6, 2026

DataPro Ta Gindaya Sharuɗɗan Da AfCRA Ke Buƙata Domin Samun Amincewar Kasuwannin Afrika

August 5, 2026
Connect with us
  • Facebook
  • Twitter
  • YouTube
  • WhatsApp
  • Instagram
  • TikTok
Top Posts
Advertisement
© 2026 ASRAH 24 MEDIA. Developed by ENGRMKS & CO..
  • Home
  • About Us
  • Contact Us
  • Privacy Policy

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.