Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufa’i, ya bayyana cewa akwai bukatar a yaba wa tsohon mataimakin shugaban kasa, Alhaji Atiku Abubakar, bisa rawar da ya taka wajen inganta tattalin arzikin Najeriya a lokacin mulkin Olusegun Obasanjo.
El-Rufa’i ya yi wannan tsokaci ne yayin da ya kai ziyarar ta’aziyya ga iyalan marigayi Edwin Clark, dattijon Neja Delta, wanda ya rasu a ranar 17 ga Fabrairu.
A yayin ziyarar, El-Rufa’i ya nuna takaicinsa kan yadda ba a cika yabawa Atiku Abubakar ba dangane da kokarinsa wajen farfado da tattalin arzikin kasar lokacin da yake mataimakin shugaban kasa daga 1999 zuwa 2007.
Sai dai, a shekarar 2016, El-Rufa’i ya zargi Atiku da yada karya da kuma goyon bayan cin hanci da rashawa. 
Wannan sabon yabo daga El-Rufa’i na zuwa ne bayan shekaru da dama na rashin jituwa tsakaninsa da Atiku, wanda ya hada da musayar kalamai kan batutuwa daban-daban na siyasa da tattalin arziki.
