Shugaban kungiyar Izala ta Najeriya, Sheikh Abdullahi Bala Lau, ya bayyana cewa shirin gudanar da babban taron Al-Qur’ani na kasa baki daya yana ci gaba, duk da sanarwar dakatarwa da aka yi a baya.
A wata hira da DW Hausa, Bala Lau ya bayyana cewa Majalisar Harkokin Addinin Musulunci ta Najeriya, karkashin jagorancin Sarkin Musulmi, ce ta shirya taron, ba wai kungiyar Izala kadai ba.
An tsara cewa mutane 30,000 ne za su halarci taron tun da farko, amma yawan mahaddatan Al-Qur’ani da suka nuna sha’awa ya haura 50,000. Wannan ya sa aka ɗage lokacin taron domin samar da ingantaccen tsari da zai hana cunkoson jama’a.
Bala Lau ya ce manufar taron ita ce tattaunawa kan matsalolin da ke damun al’umma da kuma samun hadin kai ta hanyar nazarin Al-Qur’ani. Ya kuma yi kira ga kowa da kowa da ya bayar da gudunmuwarsa wajen samun nasarar taron.
Duk da cewa wasu sun yi zargin cewa akwai siyasa a cikin shirin taron, daga bisani an fahimci cewa an shirya taron ne domin hadin kan Najeriya.
Ana sa ran taron zai gudana an Abuja, inda za a tara mahaddatan Al-Qur’ani daga sassa daban-daban na kasar. Hukumar shirya taron tana aiki tukuru wajen tabbatar da cewa an samu tsari mai kyau da zai ba kowa damar halarta cikin kwanciyar hankali da tsaro.
A karshe, Bala Lau ya yi kira ga al’umma da su ci gaba da addu’a domin samun nasarar taron, tare da fatan cewa zai zama wata hanya ta kara dankon zumunci da fahimtar juna tsakanin al’ummar Musulmi a Najeriya.
