Gwamnatin Jihar Osun ta sanar da sake biyan wani sabon kaso na tallafin kuɗi ga ma’aikatan gwamnati a faɗin jihar, a wani yunƙuri na rage musu raɗaɗin matsin tattalin arziki da kuma inganta jin daɗinsu.
Mai magana da yawun Gwamna Ademola Adeleke, Olawale Rasheed, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da aka wallafa a shafin gwamnatin jihar na X ranar Laraba.
Ya ce gwamnatin Adeleke ta ci gaba da nuna jajircewarta wajen tallafa wa ma’aikatan gwamnati, waɗanda ya bayyana a matsayin ginshiƙin gudanar da mulkin jihar.
A cewarsa, gwamnatin ta fara biyan tallafin kuɗi tun kafin aiwatar da sabon mafi ƙarancin albashi, lamarin da ya sanya Osun cikin jihohin farko da suka ɗauki irin wannan mataki.
Rasheed ya ce wannan mataki ya nuna irin ƙudurin gwamnatin wajen kula da walwalar ma’aikata da tabbatar da cewa suna samun abin da ya dace da su.
Sanarwar ta kuma kwatanta wannan gwamnati da wacce ta gabata, inda ta zargi tsohuwar gwamnatin da tauye haƙƙoƙin ma’aikata ta hanyar jinkirta biyan albashi da wasu alawus-alawus.
Gwamnatin ta jaddada cewa manufarta ita ce dawo da kwarin gwiwa a aikin gwamnati, ƙara wa ma’aikata ƙaimi, jawo ƙwararrun ma’aikata da kuma inganta ayyukan da ake yi wa al’ummar jihar.
Ta ƙara da cewa ci gaba da biyan tallafin kuɗi na daga cikin matakan da ake ɗauka domin tabbatar da ingantacciyar walwala ga ma’aikatan jihar da kuma bunƙasa ayyukan gwamnati.
