Jam’iyyun siyasa 13 masu rajista a Jihar Osun sun yi watsi da naɗin kwamitin riƙon ƙwarya na Inter-Party Advisory Council (IPAC), suna mai bayyana matakin a matsayin wanda ya saɓa wa kundin tsarin ƙungiyar.
Da yake jawabi ga manema labarai a Osogbo, shugaban Democratic Leadership Alliance (DLA) a Osun, Tosin Odeyemi, ya ce naɗin kwamitin riƙon ƙwaryar “abin dariya ne da ya wuce kima.”
Odeyemi ya bayyana cewa tun bayan ƙarewar wa’adin tsohon shugaban IPAC na jihar, Victor Akande, hukumar ta ƙasa ta gaza gudanar da sabon zaɓe saboda rashin halartar kwamitin da aka tura domin gudanar da zaɓen.
Ya ce tun daga lokacin ba a sake fitar da wata sanarwa daga hedikwatar IPAC ta ƙasa ba, amma sai aka yi wa jam’iyyun siyasa mamaki da sanarwar kafa kwamitin riƙon ƙwarya ba tare da tuntubar masu ruwa da tsaki ba.
Ya ƙara da cewa kundin tsarin mulkin IPAC bai tanadi kafa kwamitin riƙon ƙwarya ba, don haka jam’iyyun da abin ya shafa ba za su amince da wannan mataki ba.
Jam’iyyun da suka yi watsi da kwamitin sun haɗa da Labour Party (LP), African Democratic Congress (ADC), All Progressives Congress (APC), Social Democratic Party (SDP), New Nigeria Peoples Party (NNPP), Zenith Labour Party (ZLP), Action Democratic Party (ADP), Allied Peoples Movement (APM), Action Alliance (AA), African Action Congress (AAC), National Democratic Party (NDP), Nigeria Democratic Congress (NDC) da kuma Democratic Leadership Alliance (DLA).
Jam’iyyun sun kuma buƙaci Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) da kada ta amince da kwamitin riƙon ƙwaryar, suna mai jaddada cewa hanyar da aka bi wajen kafa shi ba ta dace da ƙa’idojin IPAC ba.
Ana ci gaba da sa ido kan yadda rikicin shugabancin IPAC a Jihar Osun zai kasance yayin da ake shirin gudanar da zaɓen gwamna a jihar.
