Wani ɗan Najeriya da ya dawo daga Birtaniya domin zuba jari a ƙasar, Charles Avwenagha, ya bayyana cewa yana tunanin komawa Birtaniya tare da yin watsi da fasfon Najeriya bayan Hukumar Babban Birnin Tarayya (FCTA) ta rushe wurin kasuwancinsa da ke Lokogoma, Abuja.
Avwenagha ya ce ya karɓi rancen kuɗi har fam £75,000 a Birtaniya domin gina kasuwarsa mai suna Stopover Bar and Grill, amma FCTA ta rushe ginin ba tare da ba shi wata sanarwa a hukumance ba.
A cewarsa, ya fara jin jita-jitar cewa gwamnati za ta kwato filin mako guda kafin rushewar, amma babu wanda ya ba shi takardar sanarwa ko umarnin ficewa.
Ya ce bayan ya fara kwashe kayan aikinsa, buldoza suka iso tare da rusa ginin duk da cewa ma’aikata na ci gaba da cire kayan da ke cikin wurin.
Avwenagha ya bayyana cewa kasuwancin ya samar wa mutane 84 aikin yi kai tsaye, yana mai cewa rushewar ta jefa shi cikin babban asara tare da barin ma’aikatansa babu aikin yi.
Ya kuma tambayi ko har yanzu ya dace a ci gaba da ƙarfafa ‘yan Najeriya mazauna ƙasashen waje su dawo su zuba jari, idan irin wannan abu na iya faruwa ba tare da isasshiyar sanarwa ba.
Manajan kasuwancin, Muktar Yahaya, da wasu ma’aikata sun tabbatar da cewa suna ƙoƙarin kwashe kayayyaki lokacin da jami’an rushewar suka iso tare da umartar su su bar wurin.
A nata ɓangaren, Hukumar FCTA ta ce tana ci gaba da rushe gine-ginen da aka gina ba bisa ƙa’ida ba domin dawo da tsarin babban birnin Abuja da kuma kare rayuka da dukiyoyi.
Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya sha bayyana cewa ba za a dakatar da rushe gine-ginen da suka karya tsarin birnin ba, duk da suka da koke-koken da abin ya jawo daga wasu ɓangarori.
