Abuja – Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta tabbatar da cewa Hukumar Kare Gasa da Kare Haƙƙin Masu Amfani da Kayayyaki da Ayyuka (FCCPC) na da ikon binciken korafe-korafen da suka shafi tsadar farashin tikitin jiragen sama, tana mai cewa irin wannan bincike ba yana nufin hukumar na kayyade farashi ba.
A hukuncin da Mai Shari’a B.F.M. Nyako ya yanke, kotun ta yi watsi da ƙarar da kamfanin Air Peace ya shigar yana ƙalubalantar ikon FCCPC na binciken zarge-zargen tsadar kuɗin tikitin jiragen sama.
Kotun ta bayyana cewa dokar FCCPA ta shekarar 2018 ta bai wa FCCPC ikon binciken korafe-korafen masu amfani da kayayyaki da ayyuka, kuma hakan ya bambanta da ikon kayyade farashi. Ta ce hukumar ta yi aiki cikin ikon da doka ta ba ta lokacin da ta nemi bayanai daga Air Peace bayan korafe-korafen da aka samu kan tashin farashin tikitin jiragen cikin gida a ƙarshen shekarar 2024.
Mai Shari’a Nyako ta kuma ce FCCPC ba ta umarci Air Peace ta rage farashin tikitinta ba, kuma ba ta kafa wani tsarin farashi ko ayyana cewa farashin kamfanin ya saɓa wa doka ba.
Kotun ta ƙara da cewa idan aka amince da hujjar Air Peace, hakan zai hana FCCPC binciken korafe-korafen masu amfani da kayayyaki idan ba Shugaban Ƙasa ne ya fara ba da umarnin aiwatar da tanadin kayyade farashi ba, lamarin da zai tauye ayyukan da doka ta ɗora wa hukumar.
Da yake martani kan hukuncin, Shugaban FCCPC, Tunji Bello, ya ce hukuncin ya sake tabbatar da ikon hukumar na kare haƙƙin masu amfani da kayayyaki da kuma binciken duk wani abu da ka iya cutar da masu amfani ko kuma gasa a kasuwa. Ya kuma jaddada cewa hukumar za ta ci gaba da gudanar da ayyukanta cikin adalci, gaskiya da bin doka.
