Fitacciyar jarumar fina-finan Najeriya, , ta jawo ce-ce-ku-ce bayan ta bayyana damuwarta kan matsalolin cin zarafin mata da yara da kuma wasu dabi’u da take ganin suna cutar da mata a wasu al’ummomin Igbo.
Jarumar ta ce wasu bidiyoyi da hotuna masu tayar da hankali da ta samu kwanan nan ne suka sa ta fito fili tana magana kan lamarin.
Onuoha ta jaddada cewa kasancewar namiji ne mai daukar nauyin iyali ba ya ba shi damar cin zarafi ko wulakanta mace. Ta ce mutuncin namiji yana ta’allaka ne kan halayensa nagari da rikon amana, ba wai dukiya ko matsayinsa ba.
Ta kuma soki matan da ke muzgunawa yara da ke karkashinsu, tana mai bayyana irin wannan dabi’a a matsayin cin zarafin yara wanda bai kamata a amince da shi ba ko da kuwa ana kokarin kare shi da sunan al’ada ko tsarin iyali.
Jarumar ta yi kira ga sarakunan gargajiya, shugabannin addini da sauran jagororin al’umma da su dauki matakin tattauna wadannan matsaloli a fili domin nemo mafita.
Haka kuma, ta bukaci matan da ke cikin dangantaka ko aure mai cike da cin zarafi da su nemi mafita tare da kauce wa duk wani yanayi da zai iya jefa su ko ‘ya’yansu cikin hadari.
A cewarta, akwai bukatar maza da mata su sake duba halayensu tare da hada kai wajen gina al’umma mai cike da mutuntawa da kariya ga mata da yara.
Kalaman Georgina Onuoha sun haifar da martani iri-iri a kafafen sada zumunta, inda wasu suka goyi bayan kiranta yayin da wasu suka bayyana ra’ayoyi mabambanta kan batun.
