Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ya yabawa Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), Nyesom Wike, bisa daukar kamfanin China Civil Engineering Construction Corporation (CCECC) domin gina sabuwar hanyar kilomita bakwai da ke hada al’ummomin da ke kewaye da Filin Jirgin Sama na Nnamdi Azikiwe da ke Abuja.
Akpabio ya bayyana hakan ne yayin kaddamar da aikin a madadin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.
Sabuwar hanyar ta taso daga Bill Clinton Drive zuwa yankin Tungan Madaki, kuma tana dauke da gada mai bangarori hudu da aka gina domin saukaka zirga-zirga a yankin.
Shugaban Majalisar Dattawan ya ce zabin CCECC wajen aiwatar da aikin ya ba shi kwarin gwiwa saboda irin kyakkyawan aikin da kamfanin ya yi lokacin da yake gwamnan Jihar Akwa Ibom.
Ya bayyana cewa daya daga cikin hanyoyin da kamfanin ya gina sama da shekaru 15 da suka gabata a jiharsa har yanzu tana cikin kyakkyawan yanayi ba tare da samun ramuka ba.
“Ni ma na fito daga karkara, saboda haka na san yadda ake ji idan al’umma suka shafe shekaru 37 ko 40 ba tare da hanya ba. Kamfanin CCECC ya yi min ayyuka da dama lokacin da nake gwamna, kuma daya daga cikin hanyoyin da suka gina har yanzu babu ramuka a kanta bayan shekaru 15,” in ji Akpabio.
Ya kara da cewa yana sa ran sabuwar hanyar da aka gina a Abuja za ta yi shekaru masu yawa tana cikin nagarta ba tare da lalacewa ba.
A sakon da ya wakilta Shugaba Tinubu wajen taron, Akpabio ya ce an kirkiro aikin ne domin cika alkawarin da gwamnati ta dauka wa al’ummomin da suka bayar da filayensu domin fadada titin jiragen sama na biyu a filin jirgin Abuja.
Ya ce duk da irin sadaukarwar da wadannan al’ummomi suka yi domin ci gaban kasa, sun dade ba tare da samun hanyoyi masu kyau ba.
Shugaban ya bayyana cewa aikin ba kawai hanya ba ce, har ma wata muhimmiyar hanyar bunkasa tattalin arziki da za ta inganta tsaro a kusa da filin jirgin sama tare da saukaka zirga-zirgar jama’a da kasuwanci.
Ya kuma ce gadar da aka gina a cikin aikin za ta tabbatar da ci gaba da zirga-zirga a duk shekara ba tare da tangarda ba.
Da yake jawabi a wajen taron, Ministan FCT, Nyesom Wike, ya bayyana cewa aikin na daga cikin ayyukan da ake kaddamarwa domin bikin cika shekaru uku da gwamnatin Tinubu ta yi a kan mulki.
Ya kara da cewa Hukumar FCDA ta riga ta umurci CCECC da ta ci gaba da fadada hanyar zuwa yankin Zuba domin kara amfanin tattalin arziki da zamantakewar al’umma.
Wike ya bayyana cewa aikin ya nuna kudirin gwamnatin tarayya na kai ayyukan ci gaba zuwa yankunan karkara da al’ummomin da ba su samu isasshen kulawa ba a baya.
Ministan ya kuma yabawa mazauna yankunan da aikin ya shafa saboda hadin kai da suka bayar lokacin da ake fadada filin jirgin sama.
A cewarsa, mazauna yankunan ba su nemi makudan kudade a matsayin diyya ba, sai dai samar wa matasa aikin yi da kuma gina hanyoyi.
Ya bayyana cewa gwamnatin tarayya ta riga ta cika alkawarin samar da ayyukan yi, kuma yanzu haka tana cika bangaren samar da hanyoyi.
Shi ma Babban Daraktan CCECC Nigeria Limited, Zhao ZongHe, ya ce kammala aikin cikin nasara ya samo asali ne daga kyakkyawan shugabanci da hadin kai tsakanin dukkan masu ruwa da tsaki.
Ya bayyana cewa aikin hanyar da gadar ba kawai gine-gine ba ne, har ma wata hanya ce ta hada Tungan Madaki da sauran al’ummomin yankin cikin harkokin tattalin arziki da zamantakewa na babban birnin kasa.
ZongHe ya kuma yaba wa Minista Wike saboda yadda yake sa ido kai tsaye kan aikin, yana mai cewa hakan ya taimaka wajen kammala shi kafin lokacin da aka tsara.
Ya ce sabuwar hanyar za ta inganta zirga-zirga, bude sabbin damar kasuwanci da kuma kara habaka ci gaban al’ummomin da ke kewaye da filin jirgin sama na Abuja.
