Shugaban Majalisar Dattawa, Opeyemi Bamidele, ya bayyana shirin gabatar da kudirin doka da zai sauya tsarin wa’adin shugabannin Najeriya zuwa na shekara shida guda daya kacal ga shugaban kasa da gwamnoni, bayan zaben 2027. Ya ce manufar wannan shiri ita ce rage yawan shagalolin neman sake zabe, domin shugabanni su mayar da hankali kan aiki tun daga farko zuwa karshe na wa’adinsu.
Bamidele ya bayyana hakan ne a wata hira da ‘yan jarida a ofishinsa a ranar Talata, inda ya ce tsarin na yanzu mai wa’adi biyu na jawo gwamnoni da shugabanni su shafe wani bangare mai yawa na mulkinsu suna shirin sake zabe.
Ya ce ko da yake ba kowa ne zai amince da wannan ra’ayi ba, ‘yan majalisa suna da hakkin gabatar da sauye-sauyen da suka yi imani za su inganta shugabanci da ci gaban kasa.
