Jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ta sake fuskantar gagarumin koma-baya bayan da Sanatoci biyu—Victor Umeh da Enyinnaya Abaribe—suka fice daga jam’iyyar zuwa wasu sabbin dandamali na siyasa, suna zargin rikice-rikicen shugabanci da rashin zaman lafiya a cikin jam’iyyar.
Sanata Victor Umeh mai wakiltar Anambra Central ya koma jam’iyyar Nigeria Democratic Congress (NDC), yayin da Sanata Enyinnaya Abaribe na Abia South ya shiga Labour Party (LP).
An karanta wasikun ficewar su a zauren majalisar dattawa ne ranar Talata ta hannun Shugaban Majalisa, Godswill Akpabio.
Dalilan ficewar Umeh
Umeh ya ce ya yanke shawarar ne bayan tattaunawa da iyalansa, wakilan mazabarsa da sauran masu ruwa da tsaki.
Ya ce rikicin cikin gida da shari’o’i marasa ƙarewa a ADC ne suka tilasta masa ficewa.
“Na yanke wannan shawara ne bayan shawarwari masu yawa saboda rikice-rikicen shugabanci da shari’o’i da ke ci gaba a ADC,” in ji shi.
Duk da hakan, ya ce zai ci gaba da bada gudummawa wajen ci gaban ƙasa ta sabuwar jam’iyyarsa ta NDC.
Abaribe ya koma Labour Party
Shi ma Abaribe ya tabbatar da ficewarsa daga ADC, yana mai cewa hakan ya fara aiki nan take.
Ya ce matsalolin shugabanci da rikice-rikicen shari’a a jam’iyyar ne suka sa ya yanke shawarar barin ADC.
Martanin Majalisa
Shugaban Majalisa, Godswill Akpabio, ya yi tsokaci cikin raha kan yawan sauya sheƙar ‘yan majalisa, yana mai cewa:
“Idan mutum zai riƙa sauya jam’iyya sau da yawa, sai mu daina karanta wasiku,” in ji shi cikin dariya, lamarin da ya sa aka yi dariya a zauren.
Halin siyasa
Wannan sabon sauyin ya ƙara nuna yadda ake ci gaba da sake fasalin siyasa a Najeriya, yayin da jam’iyyu ke fama da rikice-rikice da sauye-sauyen kawance gabanin zaben 2027.
