Jam’iyyar Accord Party ta musanta rahotannin da ke cewa ta goyi bayan Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, tana mai cewa har yanzu tana tsaye daram kan goyon bayan Gwamnan Jihar Osun, Ademola Adeleke, gabanin zaɓen gwamna na 2027.
Shugaban jam’iyyar na ƙasa, Maxwell Mgbudem, ne ya bayyana hakan yayin wani taron manema labarai da aka gudanar a Abuja ranar Alhamis.
A cewarsa:
“Babu wani abu makamancin haka. Wannan jam’iyya ce ta siyasa, kuma Gwamna Adeleke shi ne ɗan takararmu. Idan har akwai irin wannan goyon baya, zan tabbatar muku da cewa kafafen yaɗa labarai su ne za su fara sani.”
Ya ƙara da cewa dukkan ’yan takara za su fito ne bayan zaɓen fidda gwani, yana mai bayyana cewa jam’iyyar ta kammala taron NEC, kuma tana ci gaba da tsara yadda za a gudanar da zaɓen cikin gida.
“Muna ganin yadda masu neman takara ke tururuwa don sayen fom ɗin takara bayan mun sanar da kuɗaɗen fom da jadawalin zaɓe,” in ji shi.
Wannan bayani na zuwa ne bayan cece-kuce da ya biyo bayan wani allo (billboard) da aka kafa a Iwo, Jihar Osun, wanda ya haɗa hotunan Tinubu da Adeleke tare.
Yayin da jam’iyyar APC ta zargi Adeleke da amfani da hoton Shugaban Ƙasa domin amfanin siyasa, ɓangaren gwamnan ya musanta zargin.
Mgbudem ya nuna ƙwarin gwiwa kan nasarar Adeleke a zaɓen 2027, yana cewa:
“Kowa a ƙasar nan ya san cewa Gwamna Adeleke ya yi aiki mai kyau ƙwarai a jihar, kuma jama’a na marmarin sake zaɓensa.”
Ya kuma jaddada cewa jam’iyyar ba ta damu da adawa ba, yana mai cewa Adeleke zai yi nasara.
Haka kuma, shugaban jam’iyyar ya musanta rahotannin da ke cewa akwai rikicin shugabanci a cikin jam’iyyar.
“Domin kauce wa ruɗani, babu wani rikicin shugabanci ko ɓangare-ɓangare a cikin Accord Party, kuma babu wata umarnin kotu da ke goyon bayan Imumolen ko wani da INEC za ta bi,” in ji shi.
