Tawagar mata ta ƙwallon kwando ta Najeriya, D’Tigress, ta samu kanta a rukunin B mai matuƙar ƙarfi a gasar FIBA Women’s Basketball World Cup 2026, bayan an gudanar da jadawalin gasar a birnin Berlin.
A wannan rukuni, Najeriya za ta kara da ƙasashen Faransa, Hungary da Koriya ta Kudu, lamarin da ya sa rukunin ya zama ɗaya daga cikin mafi wahala a gasar.
Faransa, wacce ke matsayi na biyu a duniya, ana ganin ta a matsayin babbar mai jan ragamar rukunin, saboda ƙwarewarta da ‘yan wasa masu karfi da ke taka leda a manyan gasannin duniya.
D’Tigress, wacce ke matsayi na takwas a duniya, ta ci gaba da kasancewa zakaran Afirka bayan lashe kofin AfroBasket sau biyar a jere. Tawagar na ƙoƙarin tabbatar da cewa za ta iya fitar da irin wannan nasara zuwa matakin duniya.
A karkashin jagorancin koci Rena Wakama, tawagar ta nuna cigaba a tsari, horo da kuma haɗin kai a filin wasa.
Za a gudanar da gasar daga ranar 4 zuwa 13 ga Satumba, 2026 a Berlin.
