Rahotanni sun nuna cewa ɗalibar mai suna Wynnie Akakue ta rasu ne bayan wani shelf na littattafai ya fado kanta yayin da take barci a cikin aji.
Lamarin wanda ya faru a ranar 17 ga Maris ya jawo cece-kuce daga iyayen yarinyar, Dr Iasuaka Akakue da Mrs Chinyere Akakue, inda suka zargi makarantar da kokarin ɓoye gaskiya tare da neman a yi wa ‘yarsu adalci.
Bayan matsin lamba daga jama’a, gwamnatin jihar Rivers ta bayar da umarnin rufe makarantar (Campus 1, Elimgbo) har sai an kammala bincike kan lamarin.
MATSAYIN GWAMNATI
Kwamishinan Ilimi na jihar, Dr Peters Nwagor, ya bayyana cewa makarantar za ta ci gaba da kasancewa a rufe har sai an warware dukkan batutuwan da suka shafi wannan mummunan al’amari.
KOKEN MAKARANTA
Mai makarantar, Toyon Obikoya, ta ce dakatarwar ta zo musu da mamaki, amma sun amince da dokar gwamnati.
Sai dai ta roƙi gwamnati da iyayen marigayiyar da su yi sassauci, domin sauran ɗalibai da malamai suna cikin wahala.
“Waɗannan yara namu ne. Amma muna roƙon gwamnati ta tausaya mana, domin ilimin sauran yara yana cikin hatsari,” in ji ta.
Ta kara da cewa makarantar na cikin jimami kuma ta yi kokarin tuntubar iyalan yarinyar domin nuna alhini da jajantawa.
MATSAKAN SHARI’A
Ta bayyana cewa an kai batun kotu, kuma makarantar za ta bi dukkan matakan doka ba tare da hana bincike ba.
KOKEN IYAYE
Wasu daga cikin iyayen ɗalibai sun nuna damuwa kan rufe makarantar, suna cewa hakan na shafar karatun ‘ya’yansu da kuma rayuwar malamai.
Wata uwa mai suna Cynthia ta ce:
“Abin takaici ne sosai. Mun san radadin da iyayen yarinyar ke ciki, amma muna roƙon a tausaya mana mu ma.”
Wani iyaye ya kara da cewa:
“Sauya makaranta yanzu yana da wahala kuma yana da tsada. Amma muna roƙon gwamnati ta duba halin da muke ciki.”
