- Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), ya ce babu wata ƙungiya ko ɓangaren jam’iyya da ta gabatar da takardar neman amfani da Eagle Square a Abuja kamar yadda ake yadawa a wasu rahotanni.
- Wike ya bayyana hakan ne a ranar Litinin, inda ya ce labaran da ke cewa an hana wasu jam’iyyu amfani da filin taron ƙarya ne kuma ba su da tushe.
- Ya ce: “Wane ne aka hana? Ban san wani abu makamancin haka ba. Kuma ban ma san wace jam’iyya kuke magana a kai ba. Idan har jam’iyyar ADC ce, irin wannan magana nasu ne na neman tausayi.”
- Yadda tsarin amfani da Eagle Square ke aiki
- Ministan ya bayyana cewa amfani da Eagle Square Abuja na bin tsari ne na hukuma, wanda ya haɗa da gabatar da buƙata ta hukumomin da ke kula da filin da kuma biyan kuɗin da aka tanada.
- Ya ƙara da cewa babu wani buƙata da aka gabatar a hukumance ga Abuja Investments Company Limited, wacce ke kula da wurin.
- A cewarsa, duk jam’iyyun da suka taɓa amfani da wuraren taro a Abuja, ciki har da APC da PDP, sun bi tsarin da aka shimfiɗa.
- Baya ga hakan
- Nyesom Wike ya kuma bayyana cewa ayyukan gine-gine a birnin tarayya na ci gaba sosai, inda ya ce wasu manyan hanyoyi za su kammala kafin 15 ga Mayu, yayin da aikin fitilun titi zai kammala a ƙarshen watan Mayu.
- Ya ce gwamnatin FCT tana kuma shirin mayar da masu sana’o’in hannu, musamman ‘yan Apo Mechanic Village, zuwa sabbin wurare masu ingantattun kayayyaki domin inganta harkokinsu.
- Ministan ya kuma yi bayani kan barnar da iska mai ƙarfi ta yi a tashar motoci ta Kugbo, inda ya ce abin da ya faru bai kai rugujewar gini ba, sai dai an samu lalacewar rufin gini ne kawai, wanda ake gyarawa.
