Kasashe 13 sun janye ko kuma suka bayyana cewa ba za su goyi bayan sake zaben Gianni Infantino a matsayin shugaban FIFA ba, yayin da ake kara samun ce-ce-ku-ce kan shirin zaben shugaban hukumar a watan Maris 2027.
Tun farko dai sake zaben Infantino ya kasance kamar babu wata matsala, amma shirin FIFA Forward Enterprise na neman kamfanoni masu zaman kansu su zuba jari a gasar Kofin Duniya ya jawo suka daga wasu hukumomin kwallon kafa.
Daga bisani FIFA ta dakatar da shirin, yayin da Infantino ya nemi afuwa kan kura-kuran da suka biyo bayan wannan shiri.
Sai dai duk da rikicin, manyan jami’an FIFA sun sake bayyana goyon bayansu ga Infantino yayin wani taron gaggawa da aka gudanar a Rabat, Morocco.
Kasashe 13 da suka nuna adawa
Adawar ta fi karfi ne daga kasashen Turai, inda Finland ta kasance cikin kasashen farko da suka janye goyon bayansu.
Kasashen da aka bayyana cewa ba za su goyi bayan Infantino ba sun hada da:
Finland
Ingila
Wales
Serbia
Sweden
Greece
Albania
Croatia
Germany
Denmark
Netherlands
Norway
Jordan
Romania da Czech Republic su ma sun nuna alamun cewa ba za su goyi bayan Infantino ba, ko da yake ba su bayyana matsayinsu a hukumance ba.
A bangaren Jordan kuwa, shugaban hukumar kwallon kafarta, Prince Ali bin Al Hussein, ya zargi shugabancin FIFA da yin barazana wajen neman goyon baya.
Kasashen da ke goyon bayan Infantino
A daya bangaren kuma, wasu kasashe sun ci gaba da bayyana goyon bayansu ga Infantino.
Daga cikin kasashen da suka fito fili suka nuna goyon baya akwai Qatar, Sri Lanka, Kuwait, Lebanon, Morocco, Democratic Republic of Congo, Indonesia, Bhutan, Philippines, Mexico, Argentina da Paraguay.
Egypt, Niger da Mauritania su ma sun bayyana goyon baya ga Infantino, amma ba su bayar da cikakken sanarwar amincewa ba.
A halin yanzu, babu wani dan takara da ya fito fili ya bayyana cewa zai kalubalanci Infantino, yayin da wa’adin gabatar da sunayen ‘yan takara zai kare a ranar 18 ga Nuwamba.
Kowane mamba na FIFA yana da kuri’a daya
Shugabancin FIFA dai ba wai kasashe masu karfin kwallon kafa ne kadai ke yanke hukunci ba.
FIFA na da kungiyoyin kwallon kafa mambobi 211, kuma kowacce kungiya tana da kuri’a daya. Wannan na nufin kasashe kanana kamar San Marino da Bahamas suna da kuri’a irin ta manyan kasashe kamar Brazil da Ingila.
Kungiyoyin nahiyoyi kamar UEFA da CAF na iya bayyana goyon bayan dan takara tare da neman mambobinsu su mara masa baya, amma a karshe kowace kasa ce ke kada kuri’arta.
Yayin da UEFA ta nuna rashin jin dadinta da wasu matakan Infantino, Hukumar Kwallon Kafa ta Afirka, CAF, ta ci gaba da mara masa baya.
Da sauran kasashe 211 da ke da damar kada kuri’a, da kuma wa’adin gabatar da ‘yan takara bai cika ba, ana sa ran yanayin goyon bayan zai iya sauyawa kafin zaben shugaban FIFA na watan Maris 2027.
