Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya taya Mai Martaba Sarkin Kano, Khalifa Muhammadu Sanusi II, murnar cika shekaru 65 da haihuwa.
A cikin wata sanarwa da kakakin gwamnan, Sunusi Dawakin Tofa, ya fitar, Gwamna Yusuf ya bayyana Sarkin Kano a matsayin jagora mai hangen nesa, wanda hikimarsa, jajircewarsa da ƙudurinsa na tabbatar da adalci ke ci gaba da zaburar da al’umma.
Gwamnan ya yabawa Sarkin bisa gudummawar da ya bayar wajen gina ƙasa, bunƙasa ilimi, ci gaban tattalin arziki da kuma kare al’adun da addinin masarautar Kano.
Ya kuma bayyana cewa rayuwar hidimar da Sarkin ya sadaukar wa al’umma ta sa ya samu karɓuwa da girmamawa a Najeriya da ma duniya baki ɗaya.
Haka kuma, Gwamna Yusuf ya yaba da irin ƙoƙarin Sarkin wajen inganta zaman lafiya, haɗin kai, shugabanci nagari, ilimi, ƙarfafa mata da matasa, ci gaba mai ɗorewa da kuma sauye-sauyen tattalin arziki.
A ƙarshe, gwamnan ya yi addu’ar Allah Ya ƙara wa Sarkin lafiya, tsawon rai da hikima domin ci gaba da jagorantar Masarautar Kano da kuma ba da gudummawa ga ci gaban jihar Kano da Najeriya baki ɗaya.
Ya kuma jaddada aniyar gwamnatinsa na ci gaba da aiki tare da masarautar wajen aiwatar da manufofi da shirye-shiryen da za su inganta rayuwar al’ummar Kano.
